Thursday, April 30
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Har yanzu muna nan kan Bakanmu cewa, Tinubu ya sabawa doka dakatarwar da yawa Gwamnan jihar Rivers kuma muna kiran ya dawo dashi>>Kungiyar Lauyiyi ta Najeriya, NBA

Har yanzu muna nan kan Bakanmu cewa, Tinubu ya sabawa doka dakatarwar da yawa Gwamnan jihar Rivers kuma muna kiran ya dawo dashi>>Kungiyar Lauyiyi ta Najeriya, NBA

Duk Labarai
Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya, NBA ta bayyana cewa har yanzu tana nan kan bakanta dake cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sabawa doka dakatarwar da yawa gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara. Shugaban kungiyar, Afam Osigwe ne ya bayyana haka a wata hitmra da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. Ya bayyana cewa, suna kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya dawo da Gwamna Simi Fubara akan mukaminsa. Yace gwamnan rikon kwarya da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nada ba bisa doka aka nadashi ba dan haka su basu yadda dashi ba.
Kin Auren wadda kai ka fara fashe mata Dutsen Fintipio dinta na da sakamako marar kyau a rayuwarka>>Inji Fasto  Dr. Daniel Olukoya

Kin Auren wadda kai ka fara fashe mata Dutsen Fintipio dinta na da sakamako marar kyau a rayuwarka>>Inji Fasto  Dr. Daniel Olukoya

Duk Labarai
Fasto dake jagorantar cocin Mountain of Fire and Miracle Ministries (MFM), Dr. Daniel Olukoya ya gargadi musamman matasa cewa idan na miji ya zamana shine na farko da ya yi lalata da budurwa amma yaki aurenta, hakan na da illa sosai. Yace irin wadannan maza dake fashewa mata budurcinsu sannan su barsu suna cikin hadari dan kuwa rayuwarsa da budurwarnan da yawa abin ta hadu kuma abin zai ta bibiyarsa har ma ya na iya zama ya masa illa a Rayuwa. Yace da zarar mazakutar mutum ta jike a gaban mace to rayuwarsu ta hadu kenan musamman idan ya zama bai aureta ba, to lallai zai iya ganin abubuwan damuwa a rayuwarsa. Yace kuma matsalar ba lallai ta tsaya akan ka ba, zata iya bin 'ya'ya da Jikokinka.
Ji yanda Dansandan Najeriya ya bide wuta a ofishin ‘yansandan ya ķķàshè mutum daya ya kuma jikkata wasu

Ji yanda Dansandan Najeriya ya bide wuta a ofishin ‘yansandan ya ķķàshè mutum daya ya kuma jikkata wasu

Duk Labarai
Dansandan Najeriya me suna Effiong Bassey ya bude wuta a Ofishin da yake aiki na Atakpa Divisional Police dake jihar Cross Rivers inda ya kashe wata mata daya sannan ya jikkata wasu mutane 2. Lamarin ya farune da dukudukun ranar Lahadi bayan da Effiong ya koma ofis bayan ya kammala aikin dare a bankin Ekondo Microfinance Bank. Kakakin 'yansandan jihar, Ugbo Irene ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace Effiong ya nuna rashin da'a inda aka bukaci ya bayar da bindigarsa ta AK47 amma yaki. Yace ya tare kofar shiga ofishin inda ya hana shiga ko fita kamin daga baya ya bude wuta. Yace cikin mutane masu wucewa da ya harba hadda wata mata me suna Ijeoma Wilson Obot 'yar kimanin shekaru 41 da haihuwa wadda ta rasu, sauran 2 kuma suka jikkata. Yace tuni kwararrun 'yansanda suka je w...
HOTUNA DA ƊUMI-ƊUMI: KALLI YANDA ‘Yáɲ Gombe Sun Daka Wawa Ga Shinkafar Seyi Tinubu

HOTUNA DA ƊUMI-ƊUMI: KALLI YANDA ‘Yáɲ Gombe Sun Daka Wawa Ga Shinkafar Seyi Tinubu

Duk Labarai
Wasu matasa a jihar Gombe sun daka wawa kan shinkafar Seyi Tinubu. Ance motar ce ta yi faci ta tsaya sai kuma aka ankara cewa tallafin abincin Seyi Tinubu ne cike a motar, daga nan ne aka hau warwaso babu ji babu gani. Ana raɗe-raɗin cewa Seyi ya haƙura da zuwa sauran jihohin Arewa ne duba da yadda ake ta ƙorafi kan abincin da yake rabawa al'ummar Arewa. Me zaku ce?
Ya kamata a rikawa ‘yan Majalisar mu ta dattijai Gwajin shan miyagun kwàyòyì>>Sanata Natasha Akpoti ta bada shawara

Ya kamata a rikawa ‘yan Majalisar mu ta dattijai Gwajin shan miyagun kwàyòyì>>Sanata Natasha Akpoti ta bada shawara

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti ta bayar da shawarar cewa, ya kamata a rika wa 'yan majalisar Dattijai gwajin shan miyagun kwayoyi. Ta bayyana hakane a matsayin martani ga sanata Sunday Karimi wanda shima dan jihar ta Kogi ne inda ya fito yana sukarta kan fadanta da sanata Godswill Akpabio. Yace Natasha Akpoti ta jawowa jiharsu ta Kogi abin kunya sannan ta jawowa Najeriya ma abin kunya saboda abinda ta yi. Yace fadan da sanata Natasha Akpoti ta yi da Godswill Akpabio ya nuna cewa, tsohon Gwamnansu na da gaskiya akan fadan da suka yi da sanata Natasha Akpoti. A baya dai, tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello sun sha dambarwa da Sanata Natasha Akpoti. Sanata Sunday yace sun yi kokarin baiwa Sanata Natasha Akpoti baki amma taki fahintarsu.
Adamu Abdullahi Kenan, Wanda Ya Kare Da Sakamako Mafi Kyau A Jami’ar Tarayya Dake Gashua A Jihar Yobe

Adamu Abdullahi Kenan, Wanda Ya Kare Da Sakamako Mafi Kyau A Jami’ar Tarayya Dake Gashua A Jihar Yobe

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Adamu Abdullahi Kenan, Wanda Ya Kare Da Sakamako Mafi Kyau A Jami'ar Tarayya Dake Gashua A Jihar Yobe Wace fata za ku yi masa?
Sheikh Kabiru Gombe Ya Tara Wa Marayu Zunzurutun Kuɗi Har Naira Miliyan 67

Sheikh Kabiru Gombe Ya Tara Wa Marayu Zunzurutun Kuɗi Har Naira Miliyan 67

Duk Labarai
Sheikh Kabiru Gombe Ya Tara Wa Marayu Zunzurutun Kuɗi Har Naira Miliyan 67. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sheikh Muhammad Kabir Gombe, Ya Tara Wa Marayu Zunzurutun Kuɗi Har Naira Miliyan 67 Inda Ya Ke Karatun Tafsirin Al-Quran Maigirma, Cikin Wannan Watan Azumin Ramadana A Masallacin Helkwatar Ƙungiyar Izala Dake Unguwar Utako, Birnin Tarayya, Abuja, Cewar Shugaban Ƙungiyar, Sheikh Abdullahi Bala Lau Daga Jamilu Dabawa
Mahaifiyar Gwamnan Jihar Katsina ta rasu

Mahaifiyar Gwamnan Jihar Katsina ta rasu

Duk Labarai
INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIN RAJI'UN: Mahaifiyar Gwamnan Jihar Katsina ta rasu. Allah ya yima Hajiya Safara'u rasuwa yanzu, da asubahin yau lahadi 23/3/2025, mahaifiyar mai girma Gwamnan Malam Dikko Umar Radda PhD CON. Allah ya gafarta mata yasa Aljanna fiddausi ce ce makomar ta. Idan ajalinmu yazo Allah yasa mu cika da imani. Mun samu rahoton rasuwar mahaifiyar Gwamnan daga daya daga cikin jikokin marigayiyar.
Dalibai daga jami’a ta daya a Duniya watau Harvard wadda shuwagabannin kasar Amurka irin su Obama suka yi karatu a cikinta sun zo koyon sanin makamar aiki a matatar man fetur ta Dangote

Dalibai daga jami’a ta daya a Duniya watau Harvard wadda shuwagabannin kasar Amurka irin su Obama suka yi karatu a cikinta sun zo koyon sanin makamar aiki a matatar man fetur ta Dangote

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Dalibai daga jami'ar Harvard ta kasar Amurka wadda kusan itace ta daya a Duniya kuma shuwagabannin kasar Amurkar da yawa irin su Obama can suka yi karatu sun zo matatar man fetur ta Dangote sanin makamar aiki. An ga daliban ana kewayawa dasu inda suke shiga lungu da sako na matatar dan ganin yanda take aiki.