Wednesday, February 18
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Babban Abin Alfaharina shine har shekarar 2024 ta kama ta kare ban sha giya ko sau daya ba>>Inji Mawakiyar kasar Amurka, Rihanna

Babban Abin Alfaharina shine har shekarar 2024 ta kama ta kare ban sha giya ko sau daya ba>>Inji Mawakiyar kasar Amurka, Rihanna

Duk Labarai
Shahararriyar mawakiyar kasar Amurka, Rihanna ta bayyana cewa, abinda take Alfahari dashi a shekarar 2024 shine har shekarar ta fara ta kare bata sha giya ko sau daya ba. Rihanna dai ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta yayin da take murnar shigar sabuwar shekara. A kwanaki dai Rihana ta bayyana cewa ta yi nadamar shigar tsiraici da ta rika yi a baya inda tace babban abinda ya sata nadama shine da ta ga ta zama uwa.
Da Yardar Allah Shekarar 2025 Za Ta Kasance Shekarar Cika Alkawura Da Burikanmu, Sakon Shugaba Tinubu Ga ‘Yan Nijeriya

Da Yardar Allah Shekarar 2025 Za Ta Kasance Shekarar Cika Alkawura Da Burikanmu, Sakon Shugaba Tinubu Ga ‘Yan Nijeriya

Duk Labarai
SAKON SHIGA SABUWAR SHEKARA ZUWA GA 'YAN NIJERIYA Yan uwana ƴan Nigeria, A yayin da muka shiga 2025, ina yi wa kowa fatan alheri. Ina fatan mun shiga shekarar da ƙafar-dama, ƙunshe da farinciki, wadata nasara, da lafiya mai ɗorewa. Wannan sabuwar shekara da muka shiga, cike take da fatan samun ingantattun kwanaki a cikinta, kuma da yardar Allah, shekarar 2025 za ta kasance shekarar cika alkawura, da burikanmu na bai ɗaya. Duk da cewa shekarar 2024 ta kasance ɗauke da ƙalubale mai tarin yawa ga ƙasarmu da ƴaƴanta, ina da ƙwarin gwiwar cewa sabuwar shekara za ta zo mana da ƙafar -dama. Ƴar manuniya ta nuna cewa, juma'ar tattalin arzikin mu ta fara yin kyau tun daga larabarta ga al'ummarmu, farashin man fetur ya fara sauka sannu a hankali, mun sami rara a cinikayyar ƙasa da ...
Ka Çìŕè Ģìŕman Ķai Ka Saurari Koken Al’umma Kan Illolin Manufofin Haraji, Sakon Gwamnan Bauchi Ga Tinubu

Ka Çìŕè Ģìŕman Ķai Ka Saurari Koken Al’umma Kan Illolin Manufofin Haraji, Sakon Gwamnan Bauchi Ga Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Gwamnonin jam’iyyar PDP, kuma Gwmana jihar Bauchi Bala a Muhammad ya gargadi Shugaban ƙasa cewa kada ya nuna ģìŕman kai, ya kuma saurari ra’ayin al’umma akan illolin haraji. Gwamna yana mai jaddada cewa, idan aka amince da dokokin haraji da aka gabatar, hakan zai iya haifar da barazana ga ci gaban ƙananan hukumomi da jihohi. Mohammed ya soki matsayin Tinubu kan dokokin harajin da ya kira “ba na dimokuradiyya ba,” yana cewa ko wadanda suke mulkin soja za su saurari al’umma kuma su magance matsalolinsu. Kaura ya yi suka ga dokokin harajin Tinubu a gaban Majalisar Ƙasa, yana mai cewa an tsara su ne don fifita wata yanki fiye da wata.
Ni Ma Na Goyi Bayan Sarki Sanusi II Kan Batun Takaita Haihuwa, Duba Da Yadda Wasu Magidantan Ba Sa Iya Kula Da Kiwon Da Allah Ya Ba Su Na Iyalansu, Inji Sheik Pantami

Ni Ma Na Goyi Bayan Sarki Sanusi II Kan Batun Takaita Haihuwa, Duba Da Yadda Wasu Magidantan Ba Sa Iya Kula Da Kiwon Da Allah Ya Ba Su Na Iyalansu, Inji Sheik Pantami

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Ni Ma Na Goyi Bayan Sarki Sanusi II Kan Batun Takaita Haihuwa, Duba Da Yadda Wasu Magidantan Ba Sa Iya Kula Da Kiwon Da Allah Ya Ba Su Na Iyalansu, Inji Sheik Pantami Me za ku ce?
Za mu ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen da suka zama dole – Tinubu

Za mu ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen da suka zama dole – Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da bijiro da sauye-sauyen "da suka zama dole" domin gina ƙasar. Tun daga hawa mulkinsa wata 19 da suka gabata, an ga yadda Tinubu ya cire tallafin mai, ya sauya kasuwar canjin kuɗaɗen waje, ya gabatar da sabbin dokokin haraji, ya ƙaddamar da tallafin karatu, ya ƙara mafi ƙanƙantar albashi. "Za mu ci gaba da bijiro da sauye-sauyen da suka zama dole domin tabbatar da cigaba mai ɗorewa da yalwa a ƙasarmu," in ji shi cikin saƙonsa na sabuwar shekara. "Muna kan hanya mai kyau ta gina Najeriya wadda za ta kyautata wa kowa da kowa. Kada mu bari wasu 'yan tsirari daga cikinmu da ke amfani da siyasa da addini da ƙabilanci su kawar da hankalinmu."
Wahalhalun ‘yan Najeriya ba za su tashi a banza ba – Tinubu

Wahalhalun ‘yan Najeriya ba za su tashi a banza ba – Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce wahalhalu da "sadaukarwar" da 'yan ƙasar suka yi ba su tashi a banza ba tun bayan hawa mulkinsa a watan Mayun 2023. Da yake bayani cikin saƙonsa na sabuwar shekara da fadar shugaban ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce sabuwar shekarar "za ta kusanta mu da kakkyawar Najeriya da muke ta hanƙoro". A cewarsa: "Gare ku 'yan ƙasa, sadaukarwar da kuka yi cikin wata 19 da suka wuce ba ta tashi a banza ba. Ina tabbatar muku cewa kuma ba za ta tashi a banza ba nan gaba. Mu ci gaba da aikin gina ƙasa tare." Tinubu ya kuma jaddada cewa gwamnatinsa za ta ƙara mayar da hankali wajen aiwatarwa da kuma "bijiro da sauye-sauyen da suka zama wajibi" domin haɓaka tattalin arzikin Najeriya
Ya kamata Tinubu ya janye ƙudurin dokar haraji – NLC

Ya kamata Tinubu ya janye ƙudurin dokar haraji – NLC

Duk Labarai
Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya, NLC ta buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya janye ƙudurin dokar haraji da ya gabatar ga majalisar dokokin ƙasar domin bayar da dama kan sake yin nazari. Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a cikin saƙonta na sabuwar shekara, wanda shugabanta Joe Ajaero ya fitar a yau Laraba. Saƙon ya ce “domin samar da tsarin dimokuraɗiyya mai tabbatar da ci gaban ƙasa, dole ne mu gina tsari kan tubalin tattaunawa, da bai wa masu ruwa da tsaki damar tsoma baki a harkar gina ƙasa. “A kan haka ne muke sake yin kira ga gwamnatin tarayya da ta janye ƙudurin harajin da yanzu haka ke a gaban Majalisar dokoki domin bai wa duk ɓangarorin da suka dace bayar da gudumawa a kansa”. Sanarwar ta ce ƙungiyar, ita ma za ta so ta taimaka wajen samar da kyakkyawan tsarin haraji wanda zai ...
Laraba ce 1 ga watan Rajab a Najeriya – Fadar sarkin Musulmi

Laraba ce 1 ga watan Rajab a Najeriya – Fadar sarkin Musulmi

Duk Labarai
Fadar Sarkin Musulmi a Najeriya ta ayyana yau Laraba 1 ga watan Janairu a matsayin 1 ga watan Rajab na shekarar Hijira ta 1446. Wata sanarwa da Wazirin Sokoto Farfesa Sambo Wali ya fitar a daren da ya gabata ta ce Sarkin Musulmi Sa'ad Abubukar III ne ya bayyana hakan bayan ganin jaririn watan. Rajab shi ne wata na bakwai a kalandar Musulunci, wanda Hausawa ke yi wa laƙabi da watan Azumin Tsofaffi.
PDP ta nemi Tinubu ya yi bincike kan tiriliyan 25 da ta zargi ‘yan APC da sacewa

PDP ta nemi Tinubu ya yi bincike kan tiriliyan 25 da ta zargi ‘yan APC da sacewa

Duk Labarai
Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya ta PDP ta nemi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ƙaddamar da bincike kan kuɗaɗe naira tiriliyan 25 da ta zargi 'yan jam'iyyarsa ta APC da sacewa. PDP ta yi wannan kira ne a saƙon da ta wallafa na sabuwar shekara, wanda kakakinta na ƙasa Debo Ologuagba ya sanya wa hannu ranar Talata. "Ya kamata shugaban ƙasa ya wanke kansa game da yaƙi da cin hanci da rashawa ta hanyar ba da umarnin yin bincike da kuma dawo da sama da tiriliyan 25 da aka ce shugabannin APC da jami'an gwamnati sun sace," in ji sanarwar. Jam'iyyar ta kuma nemi shugaban ya bayyana adadin kuɗaɗen da gwamnatinsa ta tara daga cire tallafin man fetur da ya yi a watan Mayun 2023. Haka nan, PDP ta nemi Tinubu ya kawo ƙarshen matsalar tsaro, da yunwa, da kuma ƙarancin man fetur "domin sauƙaƙa ...
Direba ya kashe Amurkawa 10 da motarsa yayin bikin sabuwar shekara

Direba ya kashe Amurkawa 10 da motarsa yayin bikin sabuwar shekara

Duk Labarai
Aƙalla mutum 10 ne suka mutu a birnin New Orleans da ke Amurka lokacin da wata mota ta kutsa cikin dandazon mutane da asubahin ranar farko ta sabuwar shekara. Aƙalla mutum 35 ne suka samu rauni a lamarin. Ƴansanda sun ce wani mutum ne ya tuƙa wata motar a-kori-kura a guje cikin dandazon mutane a guje, da niyyar kaɗe mutane da dama. Haka nan direban motar ya buɗe wuta kan ƴansanda bayan motar tasa ta tsaya, lamarin da ya sa ya raunata jami'ai biyu. Wani jami'in Hukumar bincike ta FBI ya ce an kuma samu wani abu da ake zaton abin fashewa ne a wurin da lamarin ya faru, sai dai ya ce ba hari ba ne na ta'addanci - duk kuwa da cewa magajin garin birnin ya yi zargin hakan. An gargadi mutane su ƙaurace wa wurin da lamarin ya faru.