Gyaran Najeriya sai Allah>>Inji Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari
Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, Allah ne kadai da ya halicci Najeriya zai iya gyarata.
Ya bayyana hakane a wajan wani taron Jam'iyyar APC da ya gudana a jihar Katsina ranar Asabar data gabata inda masoyansa da yawa suka taru.
Wannan kalamai nasa sun jawo suka da Allah wadai musamman daga 'yan jam'iyyun adawa da kungiyoyin fafutuka.
Misali kakakin Jam'iyyar NNPP, Ladipo Johnson ya bayyana cewa, Jam'iyyar APC yaudarar 'yan Najeriya ta yi duk da cewa ta san bata san hanyar da zata warware matsalolin Najeriya ba amma ta karbi ragamar aikin.
Ya kara da cewa, wannan magana da tsohon shugaban kasar yayi alamace ta cewa APC ta gaza kuma ba zasu iya magance matsalar Najeriya ba inda suka jawowa kasar koma bayan tattalin arziki, ya kuma ce hakan na nuni da cewa ko...








