Tuesday, April 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bayyana Kyautar Motar Da Yara ‘Ýan Maťàñ Nan Śuke Yì, Ya Fi Illa Fiye Da Àbìnda Suke Źuwa Ýi Ake Ba Šu Motar

Bayyana Kyautar Motar Da Yara ‘Ýan Maťàñ Nan Śuke Yì, Ya Fi Illa Fiye Da Àbìnda Suke Źuwa Ýi Ake Ba Šu Motar

Duk Labarai
Daga Jamila Ibrahim Ni Wallahi yaran nan da ake bawa mota fitowa da suke yi suna nunawa ya fi illa akan abinda suke zuwa ýi ake ba su. Yanzu sun yi influencing yara kanana na ťìķțok har ya kai ga burin yarinya kawai ta yi ìşķançì a ba ta kudi, yara sun fara fandarewa. In an basu suyi hakuri su daina zuwa suna posting don yadawa duniya. Ku kuma 'yan mata da kuke kallon wadanda ake bawa gida da mota as role model har suke burge ku ku sani ba haka kawai ake ba su kudin ba, wani abun ya wuce kudin da saurayi zai bawa budurwa sabida soyayya ko sabida ya yi źìñà da ita, yawanci kudin ķùñģiya ce, bayan wasu shekaru za a a nemi wadanan dukiyar a rasa ka zama abun tausayi. Zan iya misalai da 'yan fim dayawa wadnda ma suka tare kasar waje suka yi suna, suka yi kudi amma karshen su yan...
Wata cuta data bullo ta yi sanadiyyar kwantar da mutane dubu biyar a Asibiti

Wata cuta data bullo ta yi sanadiyyar kwantar da mutane dubu biyar a Asibiti

Duk Labarai
Mutane sama da dubu biyar ne aka kwantar a Asibiti a kasar Ingila biyo bayan bullar wata cutar mura. Mutanen sun kamu da cutar ne a makon karshe na shekarar 2025 inda gadaje suka yi kadan a Asibiti sai da aka samar sa sabbin gadaje na gaggawa 1,300. An dai bayyana sunan cutar da norovirus and Respiratory Syncytial Virus (RSV) kuma yawan masu kamuwa da ita din sun fara karuwane daga ranar Kirsimeti. Daraktan hukumar kula da lafiya ta kasar, Julian Redhead ya bayyana cewa, abin damuwa ne ganin cewa mutane 5000 ake kwantara kullun a Asibiti sanadiyyar cutar. Yace kuma nan gaba lamarin zai kara munana saboda ana tsammanin sanyi ya karu. Yayi kira ga mutane su dauki matakan baiwa kansu kariya.
Gwamnatin Nasarawa ta ɓullo da shirin saka wa motocin sufuri sabon fenti

Gwamnatin Nasarawa ta ɓullo da shirin saka wa motocin sufuri sabon fenti

Duk Labarai
Hukumar karɓar haraji ta jihar Nasarawa ta ɓullo da shirin saka wa motocin sufuri sabon fenti da nufin inganta harkokin tsaro. Hukuma ta ce za a yi hakan ne kuma don ƙara yawan kuɗaɗen shiga da ake samu. Yanzu dai za a sauya wa motocin haya da keke-NAPEP launi domin a bambance tsakanin ababen hawa na haya da kuma waɗanda ba na haya ba. Launin ja ko tsanwa. Hon Moses Abeh wanda ya wakilci gwamnatin jihar a taron kaddamar da tsarin, ya ce an ɗauki aniyar yin tsarin ne domin samar da lambobin tsaro da kume fentin ga direbobi domin kare kai daga ɓata-gari da ake kira 'One Chance'. "Lambar tsaron zai kunshi bayanan direba da suka haɗa da wajen da mutum ya fito da kuma inda yake zama," in ji Moses. Ya kuma ce dole sai an san ƙungiya da direba ke ciki domin kaucewa sajewa da ɓata-g...
Rikicin kabilanci ya janyo mùtùwàr mutum tara a Jigawa

Rikicin kabilanci ya janyo mùtùwàr mutum tara a Jigawa

Duk Labarai
Wani rikici da aka danganta da kabilanci wanda ya barke tsakanin kauyukan Gululu da 'Yan-Kunama a jihar Jigawa, ya yi sanadin mutuwar mutum aƙalla tara. Rikicin ya samo asali ne sakamakon zargin da aka yi wa wasu matasan Fulani da ɓalle wani shagon kayan masarufi, inda suka yi awon gaba da wasu kayayyaki. Sai dai zuwa yanzu, an samu nasarar shawo kan rikicin wanda kuma ya janyo asarar gidaje da dama. Mai magana da yawun ƴan sandan jihar ta Jigawa, DSP Lawan Shi'isu Adam, ya shaida wa BBC cewa tuni aka aika jami'an tsaro karkashin jagorancin kwamishinan ƴan sandan jihar zuwa yankin domin kwantar da hankali. "Za mu gudanar da bincike don ganin an kama waɗanda suka aikata wannan laifi da kuma hukunta su," in ji DSP Lawan. Ya ce hankali ya fara kwanciya a garuruwan kuma jami'an ...
Yanzu-Yanzu: Yanzu muke samun Labarin Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya karbi Katin jam iyyar PDP a mazabarsa dake unguwar Sarki Kaduna

Yanzu-Yanzu: Yanzu muke samun Labarin Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya karbi Katin jam iyyar PDP a mazabarsa dake unguwar Sarki Kaduna

Duk Labarai
Rahotanni na yawo a kafafen sada zumunta cewa, tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya koma Jam'iyyar PDP. Zuwa yanzu dai babu wata sanarwa da muka samu daga PDP ko kuma shi El-Rufai data tabbatar da hakan amma maganar nata kara yaduwa a kafafen sada zumunta. Da zarar mun samun karin bayani akan hakan, zamu sanar daku..... Yanzu muke samun Labarin Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya karbi Katin jam iyyar PDP a mazabarsa dake unguwar Sarki Kaduna! Ku biyomu don kawo cikakken labarin.
Gwamnonin Arewa sun doge akan bakarsu cewa ba zasu yadda Shugaba Tinubu ya aiwatar da dokar canja fasalin Haraji ba

Gwamnonin Arewa sun doge akan bakarsu cewa ba zasu yadda Shugaba Tinubu ya aiwatar da dokar canja fasalin Haraji ba

Duk Labarai
Gamayyar gwamnonin Arewa sun sake nanata matsayarsu akan cewa ba zasu yadda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aiwatar da sabuwar dokar canja fasalin Haraji ba. Gwamnonin sun bayyana cewa, sabuwar dokar harajin zata amfani yankin Kudu ne kawai. Saidai a hirarsa da manema labarai, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa ba gudu ba ja da baya kan aiwatar da sabuwar dokar. Jaridar Punchng ta zanta da wasu daga cikin wakilan Gwamnonin Arewa inda suka bayyana mata matsayarsu game da sabon kudirin dokar. Gwamna Muhammad Yahya na jihar Gombe wanda shine shugaban kungiyar gwamnonin ta Arewa ya bayyana cewa suna nan a matsayarsu ta kin amincewa da sabuwar dokar canja fasalin Harajin. Gwamnan ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Ismaila Misilli inda yace zasu ci gaba da nun...
‘Yan kasuwar Man fetur sun baiwa gwamnatin tarayya shawarar sayar da matatun man fetur

‘Yan kasuwar Man fetur sun baiwa gwamnatin tarayya shawarar sayar da matatun man fetur

Duk Labarai
'Yan kasuwar Man fetur karkashin kungiyar,Products Retail Outlets Owners Association of Nigeria sun baiwa Gwamnatin tarayya shawarar sayar da matatun man fetur mallakar Gwamnati. Sun ce sayar da matatun zai taimaka wajan kara gasa a masana'antar ta man fetur. Sun nemi Gwamnati data sayar da matatun man fetur na Warri da Kaduna. Sun kuma baiwa gwamnantin shawarar zuba hannun jari a kasuwar gas ta CNG inda suka kuma nemi data tallafawa 'yan kasuwa 10,000 da cire tallafin man fetur ya durkusar dasu da Naira Biliyan 100 dan su tsaya da kafafunsu. Sanarwar wadda ke dauke da sa hannun shugaban kungiyar, Dr Billy Gillis-Harry ta bayyana cewa sayar da matatun man zai rage yawan kudin da Gwamnati ke kashewa.
Gwamnatin tarayya ta warewa kamfanij kera makamai na sojoji DICONS Naira Biliyan 8 duk da baya aikin azo a gani

Gwamnatin tarayya ta warewa kamfanij kera makamai na sojoji DICONS Naira Biliyan 8 duk da baya aikin azo a gani

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta warewa kamfanin kera makamai na sojojin Najaria, DICONs Naira N7,940,323,192. Kamfanin wanda aka kirkira a shekarar 1963 a samar dashine dan ya rika kerawa sojojin Najaria makamai. Hakanan dukkan gwamnatocin da aka yi a Najeriya na warewa kamfanin makudan kudade dan ingantashi, saidai har yanzu baya yin wani aikin azo a gani. Duk da kasancewar kamfanin, Har yanzu Najeriya na siyo mafi yawancin makamanta da ake amfani dasu ne daga kasashen waje.