Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi karin haske kan maganar komawarsa PDP
A dazu ne rade-radi suka watsu sosai a kafafen sada zumunta cewa, tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yanki katin shiga Jam'iyyar PDP a Unguwar Sarki Kaduna.
A wancan lokacin ba'aji wata sanarwa daga bakinsa ba ko Jam'iyyar ta PDP.
Mutane da yawa sun bayyana ra'ayoyi mabanbanta akan labarin inda wasu ke ganin hakan ba abin mamaki bane ganin yanda Gwamnatin Bola Ahmad Tinubu ta APC ta mayar da El-Rufai saniyar ware.
Idan dai za'a iya tunawa, Gwamna El-Rufai na daya daga cikin na gaba-gaba da suka dage sai Tunubu ya zama shugaban kasa kuma bayan an kafa Gwamnatin Tinubu, ya bayar da sunanshi cikin wadanda zai baiwa Ministoci amma Sai El-Rufai ya kasa tsallake tantancewar majalisa.
Tun bayan nan ne dai aka fara takun saka tsakanin El-Rufai da Gwamnatin Tinu...







