Tuesday, April 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi karin haske kan maganar komawarsa PDP

Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi karin haske kan maganar komawarsa PDP

Duk Labarai
A dazu ne rade-radi suka watsu sosai a kafafen sada zumunta cewa, tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yanki katin shiga Jam'iyyar PDP a Unguwar Sarki Kaduna. A wancan lokacin ba'aji wata sanarwa daga bakinsa ba ko Jam'iyyar ta PDP. Mutane da yawa sun bayyana ra'ayoyi mabanbanta akan labarin inda wasu ke ganin hakan ba abin mamaki bane ganin yanda Gwamnatin Bola Ahmad Tinubu ta APC ta mayar da El-Rufai saniyar ware. Idan dai za'a iya tunawa, Gwamna El-Rufai na daya daga cikin na gaba-gaba da suka dage sai Tunubu ya zama shugaban kasa kuma bayan an kafa Gwamnatin Tinubu, ya bayar da sunanshi cikin wadanda zai baiwa Ministoci amma Sai El-Rufai ya kasa tsallake tantancewar majalisa. Tun bayan nan ne dai aka fara takun saka tsakanin El-Rufai da Gwamnatin Tinu...
Kamfanin BUA yayi magana kan Kammala matatar man fetur din da yake ginawa a Akwa-Ibom

Kamfanin BUA yayi magana kan Kammala matatar man fetur din da yake ginawa a Akwa-Ibom

Duk Labarai
Kamfanin BUA ya yi karin haske kan rahotanni dake yawo suna cewa ya kusa kammala matatar man fetur da yake ginawa a jihar Akwa-Ibom. Rahotanni sun bayyana cewa, aikin gina matatar ya kai kaso 90 cikin 100. Saidai a sanarwar da kamfanin ya fitar, yace wannan ikirarin ba gaskiya bane, tabbas yana kan aikinsa na gina mamatar man fetur din wadda zara rika samar da ganga 200,000 duk kullun amma maganar an kai kaso 90 cikin 100 na ginata ba gaskiya bane. Kamfanin ya kara da cewa, bayan Mamatar man fetur din akwai kuma tashoshin gas na CNG da zai gina.
Hotuna: Hukumar NDLEA ta kama wani dan fim yana Safarar Kwàyà

Hotuna: Hukumar NDLEA ta kama wani dan fim yana Safarar Kwàyà

Duk Labarai
Hukumar hana sha da fataucin miyagun Kwayoyi NDLEA ta kama wani dan fim din Najeriya me suna Emeka Emmanuel Mbadiwe da miyagun kwayoyi. An kamashi ne ranar Juma'a, 27 ga watan Disamba na shekarar 2024. An kama Emeka ne bayan da ya aika yaronshi ya je filin jirgin sama na Murtala Muhammad dake Legas dan karbomai kwayar da aka aiko masa daga kasar Amurka. Tuni dai aka tasa keyarsa dan ci gaba da bincike.
TIRƘASHI: Na Tsani Katsalaɲdan A Rayuwata, Døn Haka Babu Wanda Ya Isa Ya Hana Ni Buɗe Gashin Kaina, Saboda Ni Yin Magana Ne Ma Ke Sa Na Yi Abu, Koda Abinda Na Yi Ba Mai Kyau Ba Ne, Muddin Za A Ce Na Daina Ni Kuma A Wannan Lokacin Ne Ma Zan Fara, Inji Jarumar Finafainan Hausa, Nafisat Abdullahi

TIRƘASHI: Na Tsani Katsalaɲdan A Rayuwata, Døn Haka Babu Wanda Ya Isa Ya Hana Ni Buɗe Gashin Kaina, Saboda Ni Yin Magana Ne Ma Ke Sa Na Yi Abu, Koda Abinda Na Yi Ba Mai Kyau Ba Ne, Muddin Za A Ce Na Daina Ni Kuma A Wannan Lokacin Ne Ma Zan Fara, Inji Jarumar Finafainan Hausa, Nafisat Abdullahi

Duk Labarai
TIRƘASHI: Na Tsani Katsalaɲdan A Rayuwata, Døn Haka Babu Wanda Ya Isa Ya Hana Ni Buɗe Gashin Kaina, Saboda Ni Yin Magana Ne Ma Ke Sa Na Yi Abu, Koda Abinda Na Yi Ba Mai Kyau Ba Ne, Muddin Za A Ce Na Daina Ni Kuma A Wannan Lokacin Ne Ma Zan Fara, Inji Jarumar Finafainan Hausa, Nafisat Abdullahi. https://www.tiktok.com/@nafisatabdullahifan/video/7455341851034275078?_t=ZM-8soiodKtVQL&_r=1 Me za ku cre?
Zan kammala gina Titin Jirgin kasan daya tashi daga Fatakwal zuwa Maiduguri kamin in sauka daga mulki>>Shugaba Tinubu

Zan kammala gina Titin Jirgin kasan daya tashi daga Fatakwal zuwa Maiduguri kamin in sauka daga mulki>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, zai kammala ginin jirgin kasan daya tashi daga Fatakwal, Jihar Rivers zuwa Birnin Maiduguri na jihar Borno kamin ya kammala wa'adin mulkinsa. Shugaban ya bayyana hakane a yayin ziyarar da ya kai jihar Enugu yayin ganawa da dattawa daga yankin kudu maso gabas. Kakakin shugaban kasar, Mr. Bayo Onanuga ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar inda yace kuma shugaban kasar yayi Alwashin samar da wata tashar makamashi a jihar Anambra.
Allah Sarki: Mata 3 da aka kama da zargin safarar kwàyà a kasar Saudiyya, an sakesu bayan an gano basu da laifi

Allah Sarki: Mata 3 da aka kama da zargin safarar kwàyà a kasar Saudiyya, an sakesu bayan an gano basu da laifi

Duk Labarai
Mata 3 'yan Najeriya da da aka kama a kasar Saudiyya aka tsare, tsawon watanni 10 bisa zargin safarar miyagun kwayoyi an sakesu bayan an gano basu da laifi. Kakakin Ministan harkokin waje, Kimiebi Ebienfa ya tabbatar da hakan. A watan Maris na shekarar 2024 ne aka kama matan a filin jirgin sama na Prince Muhammad Bin Abdulaziz dake Madina. Matan sune, Hadiza Abba, Fatima Umate Malah, da Fatima Kannai Gamboi. An kama su ne biyo bayan kama wasu 'yan Najeriya biyu da hodar Iblis. An kamasu ne bisa zargin cewa sun taimakawa masu safarar miyagun kwayoyin. Lamarin ya dauki hankula sosai a kasashen Najeriya da Saudi Arabian inda Najeriya ta shiga tsakani har aka sakesu. Bayan sakinsu, an mikasu ga ofishin jakadancin Najeriya dake kasar ta Saudiyya inda jakadan Najeriya a kasa...
MASHA ALLAH: Kakakin ‘Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Kiyawa Ya Ce Sakon Neman Shamsiyya Da Aure Da Nake Yi Ya Riske Su, Amma Sai Sun Gudanar Da Kwakkwarar Bincike Gudun Kada A Hada Tawagar Da Za Ta Fi Karfinsu Nan Gaba, Inji Dogo Yaro Crypto Yola

MASHA ALLAH: Kakakin ‘Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Kiyawa Ya Ce Sakon Neman Shamsiyya Da Aure Da Nake Yi Ya Riske Su, Amma Sai Sun Gudanar Da Kwakkwarar Bincike Gudun Kada A Hada Tawagar Da Za Ta Fi Karfinsu Nan Gaba, Inji Dogo Yaro Crypto Yola

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kakakin 'Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Kiyawa Ya Ce Sakon Neman Shamsiyya Da Aure Da Nake Yi Ya Riske Su, Amma Sai Sun Gudanar Da Kwakkwarar Bincike Gudun Kada A Hada Tawagar Da Za Ta Fi Karfinsu Nan Gaba, Inji Dogo Yaro Crypto Yola A baya dai, Dogo Yaro Crypto Yola ya dauki hankula bayan da ya fito da gaske yace yana son Shamsiyya duk da halin data tsinci kanta. Da yawa sun yi mamaki da wannan karfin hali nashi.
An kaiwa Tawagar Hadimar Gwamnan Kaduna hari

An kaiwa Tawagar Hadimar Gwamnan Kaduna hari

Duk Labarai
Hadimar gwamnan jihar Kaduna dake bashi shawara akan harkokin siyasa, Hon. Rachael Averik ta tsallake rijiya da baya a yunkurin kisheta da aka yi. An kaiwa tawagar Hon. Rachael Averik harin kwantan baunane ranar Alhamis, 2 ga watan Janairu. Harin ya farune a tsakanin kauyukan Tsauni Majidadi da Gani dake karamar hukumar Sanga ta jihar. A ranar tana kan hanyar zuwa Gwantu ne abin ya faru. A ranar taje gaisuwane sannan ta kaddamar da Asibitin da Alhaji Muhammad Umar Numbu ya gina a masarautar Arak. Jami'an tsaron dake tare da ita sun budewa maharan wuta inda anan aka jikkata direbanta da Dansanda daya. Jami'an tsaro a jihar sun fara bincike kan lamarin. Gwamnatin jihar ta yi Allah wadai da harin.

Maganin hana karyewar gashi

Magunguna
Abubuwan dake haddasa Karyewar gashi sun hada da yawan damuwa, zafi, ciwo me tsanani irin su ciwon suga, hawan jini da sauransu. A wannan rubutu zamu yi cikakken bayani game da karyewar gashi da maganin hana karyewar gashi. Bushewar gashi da barinshi ba gyara ma yana sawa ya rika kakkaryewa. Ga cikakken bayani kamar haka game da abubuwan dake kawo karayar gashi: Abinci: Kalar abincin da ake ci na taimakawa matuka wajan kyawun gashi da kuma hana karyewarsa. Kalar abincin dake taimakawa wajan hana karyewar gashi sune, dafaffen kwai, gasashshiyar kaza, ganye irin su kabeji, dodon kodi, madara, da Yegot. Yawan Damuwa: Kasancewa cikin yawan damuwa na sanya karyewar gashi. Dan haka, masana sun bada shawarar a rika cire kai daga cikin damuwa dan samun gashi me kyau da baya karyewa....