Rahotanni sun bayyana cewa, Ana ta rabu zuwa gida 4 a Jos dake jihar Filato.
Lamarin ya farune ranar Laraba, kamar yanda Leadership Hausa ta ruwaito.
https://twitter.com/i/status/2018976625699037409
Wata Kirista ta bayyana cewa tana son mawaki OGAbbah wanda dalilin haka ya sanya ta musulunta.
Ta bayyana masa hakane a comment bayan da ya wallafa Bidiyon wannan wakar a shafinsa na Tiktok.
OgAbbah dai shine yayi wakar samu kudinka kawai ka kashe wadda ta watsu sosai a ciki da wajen Najeriya.
Ya tambayeta cewa da gaske take abinda ta fada? Inda tace masa Eh da gaske take.
yace to ta aika masa da DM
https://www.tiktok.com/@ogabbah/video/7600814482528423186?_r=1&_t=ZS-93dZwrc6liT
Tauraron Mawakin Hausa, Soja Boy ya bayyana cewa, kudin da ya mallaka sun fi karfin Naira Biliyan 2.
Ya bayyana hakane a hirar da Ali Jita yayi dashi inda yace dan haka dole yayi abinda yake so.
https://www.tiktok.com/@arewa_realistic/video/7602534368900369682?_r=1&_t=ZS-93dXULQenhY
Hakanan ya kara da cewa, Mawaki, Wizkid yafi Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa.
Yace yanzu da Wizkid zai ce yana son ganawa da sarkin Saudiyya wani Malami yace yana son ganawa da sarkin, sai Wizkid ya riga malamin ganawa da sarkin.
https://www.tiktok.com/@mr_ceedking/video/7602463541144177940?_r=1&_t=ZS-93dZ8iLRUH3
Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka ta aiko da sojoji zuwa Najeriya.
Kafar Reuters ta bayyana cewa an aiko da sojojin na musamman zuwa Najeriya dan su taimaka wajan samar da tsaro.
General Dagvin R.M. Anderson wanda shine shugaban rundunar sojojin Amurka a Afrika ya tabbatar da hakan.
Ya bayyana cewa, sojojin ba masu yawa bane amma bai bayyana ko guda nawa bane.
Sannan zuwa yanzu ba'a bayyana wace jihace aka tura sojojin.
Tsohon dan majalisar tarayya daga jihar Jigawa, Hon. Gudaji Kazaure kenan a wannan Bidiyon yake yawo a kafa yana hira da jama'ar gari.
Da yawa sun ce da bai aikata abin a zo a gani ba da bai isa yayi hakan ba.
https://www.tiktok.com/@auwaluadamubaffa/video/7602350055772720391?_r=1&_t=ZS-93cg2ontX3w
Tauraruwar Tiktok, Habiba Dorayi ta bayyana cewa, dalilin da yasa ta daina Tallar maganin Karfin maza shine, wadanda ke zuwa saye sai su ce zasu gwada.
Tace dalili kenan da yasa ta shafawa kanta lafiya ta daina sayar da maganin karfin mazan.
https://www.tiktok.com/@habibadorayi/video/7602657731538947344?_r=1&_t=ZS-93cffpKccGe
Wata 'yar Najeriya dake zaune a Saudiyya ta bayyana cewa, Malam Rigi-Rigi ya kammala tallar shirka ya koma ga Allah.
Tace ya kammala tallar shehunnai amma yanzu ya koma ga Allah.
Tace Allah ya jikan Musulmi.
https://www.tiktok.com/@useryardubaitarasulu/video/7602478845060599047?_r=1&_t=ZS-93cev3vlUq8
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar EFCC sun kama Samha M Inuwa.
An kamata ne dalilin wani Bidiyo data wallafa tana share Majina da Kudi.
Bidiyon ya watsu sosai a kafafen sada zumunta.
Hukumar EFCC tace Samha M. Inuwa na hannunsu suna Bincike akanta.
https://www.tiktok.com/@garkuwanjarumigrowhost/video/7601978517642874119?_r=1&_t=ZS-93cciqizaPQ
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC sun kama Tauraruwar fina-finan Hausa, Sàmha M. Inuwa.
An kama ta ne bayan da wani Bidiyonta ya yadu tana share majiya da takardar kudin Naira.
EFCC tace bayan yaduwar Bidiyon, ta bibiyi Samha inda ta kamata
Hukumar tace yanzu haka Samha na hannun EFCC ana bincike.
Wani Bidiyon sanata Adams Oshiomhole da aka gani yanawa wata mata Tausa ya dauki hankula.
An ga Bidiyon da ya dauki hankula a kafafen sada zumunta ana ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi akai.
https://twitter.com/i/status/2018444261998629061