Friday, July 3
Shadow

Duk Labarai

Muna da Hujjojin cewa kun aikata laifin cin amanar kasa amma dai Tausayine yasa muka yafe muku>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa kananan yaran da ta yiwa Afuwa

Muna da Hujjojin cewa kun aikata laifin cin amanar kasa amma dai Tausayine yasa muka yafe muku>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa kananan yaran da ta yiwa Afuwa

Duk Labarai
Kananan yaran da aka kama aka gurfabar a kotu bisa zargin cin amanar kasa da yunkurin kifar da gwamnatin shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu amma Shugaban ya yafe musu sun koma gida Kano. Kamin komawarsu, sai da suka je fadar shugaban kasa suka gana da mataimakin shugaban kasar, Kashim Shettima inda ya bayyana musu cewa suna da Bidiyo da hotuna dake nuna cewa sun aikata laifi amma tausayi irin na shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne yasa ya yafe musu. Ya bayyana cewa zanga-zangar tsadat rayuwa ta jawo asarar Naira Biliyan 300. Ya jawo hankalin matasan da cewa kada su yadda ayi amfani dasu wajan tayar da fitina inda yace wannan dama ce da suka sake samu ta su zama na gari. Tuni dai aka mika su hannun gwamnan jihar ta Kano Abba Kabir Yusuf ina shima ya daukesu zuwa gida.
Najeriya ta fada Duhu yayin da matsalar wutar lantarki ta sake aukuwa, Ji Jihohinnda lamarin ya shafa

Najeriya ta fada Duhu yayin da matsalar wutar lantarki ta sake aukuwa, Ji Jihohinnda lamarin ya shafa

Duk Labarai
'Yan Najeriya sun fada duhu biyo bayan sake samun matsala da wutar lantarkin kasar ta yi. Wannan shine karo na 3 da wutar lantarkin kasar ke samun matsala a shekarar 2024. Da Misalin karfe 1:50 pm. Na ranar Talata ne wutar lantarkin ta sake samun matsala. Kamfanin kula da wutar na kasa,TCN ya tabbatar da hakan amma yace ba gaba daya wutar bace ta samu matsala. Kakakin hukumar, Ndidi Mbah ne ya tabbatar da hakan inda yace injiniyoyinsu na aiki tukuru dan dawo da wutar. Ya kara da cewa An samu dawo da wutar a babban birnin tarayya Abuja kuma suna kokarin dawo da ita a sauran jihohi.
Bayan da ya tsere daga Najeriya, Dan Daudu Bobrisky ya wallafa Bidiyo yana kirga daloli

Bayan da ya tsere daga Najeriya, Dan Daudu Bobrisky ya wallafa Bidiyo yana kirga daloli

Duk Labarai
Shahararren dan daundu, Bobrisky wanda ya sha dambarwar kame daga hukumomin Najeriya amma daga baya ya samu tsallakewa zuwa kasar waje ya sake bayyana. Ya wallafa hotunan Bidiyo yana wasa da dalolin Amirka. https://twitter.com/Chrisvlognation/status/1853869625794302249?t=oy2yERZfQhy_nqkrTmyhlw&s=19 Wani har ya tsokaneshi da cewa aro kudin yayi amma ya mayar masa da martanin cewa a Najeriya ne ake iya yin haka amma banda kasar waje. Bobrisky ya kara da cewa, Wani masoyinsa ne ya bashi wadannan kudade.
Jami’in Hukumar NSCDC ya yanke jiki ya fadi ya mutu jim kadan bayan da aka masa karin girma

Jami’in Hukumar NSCDC ya yanke jiki ya fadi ya mutu jim kadan bayan da aka masa karin girma

Duk Labarai
Jami'in hukumar tsaro ta NSCDC Opatola wanda ba'a dade da karawa mukami ba ya yanke jiki ya fadi ya mutu jim kadan bayan an biyashi Albashi. Yana aiki ne a Iwo kuma ya mutu ne bayan da ya shiga ban daki kamar zai biya bukatarsa. Wasu shaidu sun bayyanawa jaridar The Nation cewa mutumin ya je wajan aiki lafiya kalau a ranar da ya mutu. Abokan aikinsa sun ce sun ga Albashinsu suna korafi akai jim kadan kawai aka ce ai ya mutu.
Mataimakin shugaban kasa Kashin Shettima ya mika matasan da Gwamnati tawa Afuwa zuwa ga Wakilan jihohinsu

Mataimakin shugaban kasa Kashin Shettima ya mika matasan da Gwamnati tawa Afuwa zuwa ga Wakilan jihohinsu

Duk Labarai
Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Sen. Kashim Shettima ya jagoranci bayar da Matasa yan asalin Jihar Kano zuwa ga Wakilan Jihar Kano a Gwamnatin Tarayya wanda suka hada Shugaban kwamitin kasafin kudi na Majalisar Tarayya, Hon. (Dr. Abubakar Kabir Abubakar Bichi, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai Sanata Barau I Jibril da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf domin dawowa dasu wajen Iyayensu.
Kalli Bidiyo yanda Abba Kabir Yusuf ya sauka daga kujera ya baiwa Kwankwaso ya zauna

Kalli Bidiyo yanda Abba Kabir Yusuf ya sauka daga kujera ya baiwa Kwankwaso ya zauna

Duk Labarai
An ga wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta inda aka ga gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya baiwa Tsohon gwamnan jihar, Rabiu Musa Kwankwaso kujerar da yake zaune dan ya zauna. Hakan na zuwane yayin da rahotanni ke yawo cewa an samu baraka a tsakanin Gwamna Abba Kabir Yusuf da Kwankwason. https://www.youtube.com/watch?v=EfYjJ3F6vgM A jiya dai hutudole ya kawo muku rahoton cewa, Jaridar Daily Nigerian tace Abba ya daina daukar wayar Kwankwaso.