A hukumance Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya fice daga jam'iyyar ADC ya koma jam'iyyar NDC.
An ga Kwankwaso da Peter Obi suna shiga ofishin jam'iyyar NDC dan su yi rijista.
https://twitter.com/i/status/2050973050514915460
A dazu ne rahotanni suka yi yawa musamman a kafafen sada zumunta cewa, Jam'iyyar APC a jihar Kano, ta hana Alhassan Ado Doguwa takarar kujerar majalisar wakilai.
Lamarin ya zowa mutane da yawa da mamaki ganin cewa ya shafe shekara da shekaru yana rike da wannan kujerar.
Saidai wani Bidiyo ya bayyana a kafafen sadarwa inda aka ji yana sukar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf kan cewar da yayi Kullu Nafsin Zalikatul Maut.
Doguwa yacw abin kunyane ga jihar Kano a ji Gwamnanta ya fadi irin wannan maganar yana dan musulmi.
https://twitter.com/i/status/2050926399045660896
Da yawa sun alakanta cewa wannan magana da Alhassan Ado Doguwa yayi ce tasa aka hanashi tikitin tsayawa takarar majalisar wakilansa.
Jam'iyyar NDC ta bayyana cewa, a yau, Lahadi, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi zasu shiga cikin jam'iyyar.
Jam'iyyar ta sanar da hakane ga manema labarai kamar yanda shahararren dan jarida daga gidan talabijin na Arise TV, Rufai Oseni ya sanar.
Yace Duka Peter Obi da Kwankwaso zasu bar ADC su koma jam'iyyar NDC kamar yanda jami'iyyar ta NDC ta sanar dasu.
Tuni dai Peter Obi ya sanar da ficewa daga jam'iyyar ADC.
Rahotanni sun bayyana cewa, Peter Obi ya fice daga jam'iyyar ADC.
Peter Obi ya bayyana hakanne a shafinsa na X.
Yace abinda ya koroshi daga jam'iyyar Labour Party ne ya iske a jam'iyyar ADC shiyasa ya yanke shawarar fita daga cikinta
Yace har yanzu yana girmama Atiku Abubakar da shugaban jam'iyyar, David Mark.
Yace ba wai son neman takarar shugaban kasa ko ta mataimakin shugaban kasa ko ta kakakin majalisa ne yasa ya fice daga ADC ba.
Yace ya ficene domin ganin an gyara Najeriya kowa yana jin dadi babu yunwa babu talauci.
Jam'iyyar ADC ta sanar da ranar da zata yi zaben fidda gwani na jam'iyyar.
Za'a fara zabenne daga ranar 21 ga watan Mayu inda za'a yi na 'yan majalisu sai na gwamnoni da za'a yi ranar 22 ga watan Mayu, sannan a yi na shugaban kasa ranar 25 ga watan Mayu.
An ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya kaiwa tsohon Ministan sufuri Rotimi Amaechi ziyara har gida.
Saidai Atiku ya zauna yana jiran Amaechi a falonsa Amaechin bai fito ba sai da aka dan jima
Hakan yasa wasu ke cewa Abinda Amaechin yayi bai kyauta ba.
https://twitter.com/i/status/2049505973803339838
Tsohon Gwamnan jihar Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa irin rikicin da yasa sua bar jam'iyyar NNPP yanzu haka ya mamaye jam'iyyar ADC.
Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta shafinsa na sada zumunta inda yace dan hakane suka fara neman jam'iyyar da zasu sake komawa dan ci gaba da fafutuka.
Yace a yanzu haka suna magana da jam'iyyar NDC da PRP.
Kwankwaso yace kuma maganar fitowa takarar shugaban kasa ko goyon bayan wani dan takarar shugaban kasa duk babu gaskiya a cikinsu.
Sannan yace da ba'a ganshi ba a wasu tarukan jam'iyyar ADC, wani uzuri ne ya hanashi kuma ya sanar da shugabancin jam'iyyar.
Farfesa Hon. Sheikh Isa Ali Pantami ya goge wani Bidiyo da aka gani a shafinsa na wani Malami yana cewa, duk wanda ba ya son takarar Pantamin Munafuki ne.
Bayan ganin Bidiyon a shafinsa na Facebook, mutane da yawa ciki hadda masoyan malam din sun yi Allah wadai da wallafa wannan Bidiyon wanda da yawa suka ce bai dace ba.
Daga baya an goge Bidiyon daga shafin inda aka sake yin wani Rubutu cewa, ba Farfesa Pantami ne ya wallafa Bidiyon ba sannan bai amince da kalaman cewa duk wanda baya sonsa Munafuki ne ba.
Yace ya fahimci a siyasa suka na daga cikin manyan abubuwa masu amfani da ke karkato hankalin mutum yayi gyara.
https://twitter.com/i/status/2050651416486613183
My attention has been drawn to a post on this page by one of the admins, containing a strongly worded message ...
Wannan wata budurwa ce da ta bar makaranta ta je wajan Saurayinta.
Saidai bayan sun kammala holewa, budurwar ta rigamu gidan gaskiya.
Lamarin ya tayar da hankali a kafafen sadarwa.
https://twitter.com/i/status/2050583494682616254
Bidiyon yanda Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya je masallacin Juma'a a makare ya dauki hankula.
An ga ya bi sahu a wajan masallacin, ba'a ture mutane ya shiga cikin masallacin ba.
Lamarin ya dauki hankulan mutane sosai inda akai ta yaba masa, wasu ke cewa bashi da girman kai.
https://www.tiktok.com/@realhishamabba/video/7635013366934686997?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7635013366934686997&source=h5_m×tamp=1777730423&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=76251836750013...