Friday, February 13
Shadow

Duk Labarai

An fara: Ji shaguben da Hadimin Gwamnan Kano yawa Kwankwaso da ya dauki hankula sosai

An fara: Ji shaguben da Hadimin Gwamnan Kano yawa Kwankwaso da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Me baiwa Gwamnan Kano shawara akan harkokin kafafen sada zumunta, Salisu Yahaya Hotoro ya yi wani Rubutu da ake zargin da Kwankwaso yake, duk da bai kira suna ba. Ya rubuta cewa, Kwanannan mutane zasu fahimci wanene ya ci amanar mutanen Kano kuma wanene ya tsaya tare dasu yake kare muradinsu. Yace dambarwa irin ta Novemed, data Scholarship, da dambarwar sayar da filaye, dambarwar tsaftace ruwan Kano, da sauran rikita-rikitar cin hanci da Rashawa sune suka kawo mu matsayin da ake yanzu. Kamar yanda Imran U. Wakili ya ruwaito(@IU_Wakilii) https://twitter.com/i/status/2016428116692849077
Kasuwar Onitsha zata ci gaba da kasancewa a kulle har na tsawon sati daya>>Inji Gwamna Soludo

Kasuwar Onitsha zata ci gaba da kasancewa a kulle har na tsawon sati daya>>Inji Gwamna Soludo

Duk Labarai
Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya sake nanata cewa, Kasuwar Onitsha zata ci gaba da kasancewa a kulle har na tsawon sati daya. Yace idan kuma litinin ta zo 'yan kasuwar suka ki budewa, kamar yanda suka saba, zai sake kulleta na tsawon sati biyu. Yace tunda hutu suke so, zai taimaka musu su huta da kyau. Hakanan yace idan aka ci gaba da kulle kasuwar, zai kwace shagunan masu kulle shagonsu ya baiwa wadanda suka shirya yin kasuwanci. https://twitter.com/i/status/2016503952573862074 Hakan na zuwane yayin da 'yan kasuwar suka fito suka tare babbar gadar Onitsha suka hana shiga da fita daga garin.
Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un: Jirgin saman Sojojin Najeriya ya kara yin kuskure akan farar Hula

Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un: Jirgin saman Sojojin Najeriya ya kara yin kuskure akan farar Hula

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Naija na cewa, jirgin sojin saman sojojin Najeriya ya sake kuskurewa akan farar hula a jihar Naija. Lamarin ya farune a Kurgi dake karamar hukumar Kuriga. Lamarin ya farune ranar 25 ga watan Janairu wanda ya yi sanadiyyar jikkatar mutane da dama. An jima dai ana samun irin wannan kuskuren akan farar Hula a Najeriya.
Kalli Bidiyon matakin da ‘yan Kasuwar Onitsha suka dauka bayan da Gwamnan jihar ya kulle kasuwar saboda suna kin fitowa kasuwa ranar Litinin

Kalli Bidiyon matakin da ‘yan Kasuwar Onitsha suka dauka bayan da Gwamnan jihar ya kulle kasuwar saboda suna kin fitowa kasuwa ranar Litinin

Duk Labarai
A jiyane da muka kawo muku Rahoton cewa, Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya kulle kasuwar Onitsha na tsawon sati daya. Dalili shine 'yan kasuwar na biyewa tshageran dake hanasu bude shaguna ranar Litinin. A martanin 'yan kasuwar, sun je gadar Onitsha inda suka ajiye motocinsu suka hana shiga da fita garin dan nuna fushinsu da matakin da gwamnan ya dauka. https://twitter.com/i/status/2016412406876897514
Kalli Bidiyon: Na shiga Musulunci amma abin mamaki Musulmai sai Izgili suke min suna cewa Musuluncin karya nake, da gayamin Munanan Kalamai>>Inji Maryam Zool

Kalli Bidiyon: Na shiga Musulunci amma abin mamaki Musulmai sai Izgili suke min suna cewa Musuluncin karya nake, da gayamin Munanan Kalamai>>Inji Maryam Zool

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Maryam Zool wadda tace ta shiga Musulunci ta bayyana cewa ta hadu da abinda bata yi tsammani ba. tace tasha Kiristoci ne zasu rika mata Izgili amma sai gashi Musulmai ne suka rika zaginta da gaya mata Arniya da cewa wai Musuluncin qarya take. Tace dan haka yanzu ta koma Kirista. https://www.tiktok.com/@fcbaby246/video/7599853844775898386?_r=1&_t=ZS-93Rrsm6AzWz
Kalli Bidiyon: Dalilin da Abba ya bayar na komawarsa APC ya sa mutane rike baki

Kalli Bidiyon: Dalilin da Abba ya bayar na komawarsa APC ya sa mutane rike baki

Duk Labarai
An wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta, anga Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf na bayyana cewa ba'a ja da Gwamnatin tarayya. Ya bayyana cewa, kudaden shiga da suke samu daga gwamnatin tarayya ne suke amfani dasu wajan yiwa al'umma aiki. https://twitter.com/i/status/2016272428893151566 Wasu sun fassara wannan kalami nasa da cewa, ashe kudi ne suka sanya ya koma jam'iyyar APC din.