Kalli Bidiyon mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima yana cewa, ‘Yan Najeriya kun yi sa’a da Allah ya baku ni a matsayin mataimakin shugaban kasa
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa 'yan Najeriya sun taki sa'a da Allah ya basu shi a matsayin mataimakin shugaban kasa.
Ya bayyana hakane a ziyarar da ya kai jihar Katsina.
Da yake jawabi, Kashim Shettima yace Katsinawa sun yi dace da Allah ya basu Dikko Raddah a matsayin gwamnan, yace a tafa masa.
Sannan yace 'yan Najeriya kuma sun yi dace da Allah ya basu shi a matsayin mataimakin shugaban kasa.
https://www.tiktok.com/@kashiimshettima/video/7563681781183040776?_t=ZS-90js9tRs0Zd&_r=1








