Friday, February 27
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyo: Da Kare da Alade duka ba Najasa bane>>Inji Sheikh Maqari

Kalli Bidiyo: Da Kare da Alade duka ba Najasa bane>>Inji Sheikh Maqari

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Ibrahim Maqari ya bayyana cewa da kare da Alade duka ba najasa bane. Ya bayyana hakane bayan wata tambaya da aka masa cewa, karene ya taba jikin wani mutum. Malam yace kare yana kamo dabba, watau ana zuwa dashi farauta ya kamo dabba kuma a ci, yace dan haka ba najasa bane. Malam ya kara da cewa, har Alade ma ba najasa bane. https://www.tiktok.com/@binyusuf37/video/7554864115823430920?_t=ZS-90H29wUGzFQ&_r=1
Kalli Bidiyon:An kama wani magidanci Da ya Dirqawa diyarsa cikin shege a jihar Yobe

Kalli Bidiyon:An kama wani magidanci Da ya Dirqawa diyarsa cikin shege a jihar Yobe

Duk Labarai
Wani Magidanci me suna Umar Maigoro ya shiga hannun jami'an tsaro bayan dirkawa diyarsa ciki. Yarinyar me shekaru 16, ya mata karyar cewa, bashi ne ya haifeta ba inda yace ida shegiya ce mahaifiyarta ta je gidansa da itane shi kuma ya rene ta. Saidai da ciki ya shiga sun yi kokarin zubar dashi amma sai Asiri ya tonu. Kalli Bidiyon jawabinsa a kasa: https://www.tiktok.com/@sirkhamerl/video/7556744491114384648?_t=ZS-90H0utX9l5d&_r=1
Wallahi idan na Rubutawa Sheikh Guruntum shafi guda na Larafci ba bu wasali ya iya karantawa daidai na yadda ya zama malamina>>Inji Malam Abdulfatahi Sani Tijjani

Wallahi idan na Rubutawa Sheikh Guruntum shafi guda na Larafci ba bu wasali ya iya karantawa daidai na yadda ya zama malamina>>Inji Malam Abdulfatahi Sani Tijjani

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Malam Abdulfatahi Sani Tijjani ya bayyana cewa, Idan ya rubutawa Sheikh guruntum Larabci shafi daya babu wasali ya karantashi babu matsala ya yadda ya zama malaminsa. Ya bayyana hakane a wajan wani Karatu da ya gabatar inda yake kalubalantar malamai dake goyon bayan Malam Lawal Triumph. https://www.tiktok.com/@habibou.adamou..227/video/7556791540681673995?_t=ZS-90GYvK8ssNN&_r=1
Tambaya: Matar aure ce ta gayyaceni zuwa gidanta tace mijinta baya iya biya mata bukata amma yace yas yafe mata ta nemi wanda zai biya mata bukata shine na yi

Tambaya: Matar aure ce ta gayyaceni zuwa gidanta tace mijinta baya iya biya mata bukata amma yace yas yafe mata ta nemi wanda zai biya mata bukata shine na yi

Duk Labarai
Wani mutum ya aikawa Malam Aminu Ibrahim Daurawa da tambayar cewa, wata matar aure ta gayyaceshi gidanta ta nemi yayi lalata da ita. Tace masa mijinta baya iya biya mata bukata, amma yace ya yafe mata ta nemi wani ya rika biya mata bukata. Yace yayi amma yana tambayar shin yana da zunubi ganin cewa Mijin yace ya yafe? Saurari amsar Malam a Bidiyon kasa: https://www.tiktok.com/@nurasara531/video/7557091029283818760?_t=ZS-90GHgohPxth&_r=1
Sojoji kadau ba zasu iya magance matsalar tsaron Najeriya ba>>Inj Shugaban Sojoji, Janar Christopher Musa

Sojoji kadau ba zasu iya magance matsalar tsaron Najeriya ba>>Inj Shugaban Sojoji, Janar Christopher Musa

Duk Labarai
Shugaban Hedikwatar tsaro ta kasa, Christopher Musa ya bayyana cewa, Sojoji kadai ba zasu iya magance matsalar tsaro a Najeriya ba. Ya nemi hadin kan al'umma wajan magance matsalar tsaro ta kungiyar B0k0 Hàràm. Ya bayyana hakane a Abuja wajan kaddamar da littafin tsohon shugaban hedikwatar tsaro, Lucky Irabor. Yace aikin sojoji wajan samar da tsaro baya wuce kaso 25 zuwa 30. Yace hadin kai na da muhimmanci sosai wajan magance matsalar tsaro. Ya bayar da misali da kasar Singapore wadda yace sun samu ci gaban matsalar tsaro ne ta hanyar hadin kai da son juna, inda yace Najeriya ma sai an yi akan.
Najeriya ta zo ta biyu a yawan mutane matalauta a Duniya

Najeriya ta zo ta biyu a yawan mutane matalauta a Duniya

Duk Labarai
Tsohon shugaban Hukumar kididdiga ta kasa, NBS, Yemi Kale ya bayyana cewa, Najeriya ce ta biyu bayan India da ta fi kowace lasa yawan matalauta. Yace akwai matalauta Miliyan 89 a Najeriya wanda hakan yana nufin kaso 40 na 'yan Najeriya matalauta ne. Ya bayyana hakane a cikin sakoshi na ranar 'yanci. Yace babban abinda ke kawo Talauci shine yanda gwamnati bata yin tsare-tsare masu kyau.
Ku kara Hakuri da shugaba Tinubu an kusa fara cin ribar wahalar da ake sha>>Inji Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio

Ku kara Hakuri da shugaba Tinubu an kusa fara cin ribar wahalar da ake sha>>Inji Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio

Duk Labarai
Kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio ya baiwa 'yan Najeriya hakuri inda yace su kara dariya kan wahalar da ake sha inda yace dadi na nan tafe. Akpabio ya ce suna sane da irin wahalar da ake sha dan haka suke ara baiwa mutane hakuri, yace tuni har matakan da gwamnatin Tinubu ta dauka sun fara samar da sakamako me kyau. Ya bayyana hakane a sakonsa na ranar 'yancin Najeriya.