Monday, March 2
Shadow

Duk Labarai

Mun cimma yawan kudin shigar da muke bukata na gaba dayan shekarar 2025 a watan Augusta kuma ba ta hanyar Man fetur ba>>Inji Shugaba Tinubu

Mun cimma yawan kudin shigar da muke bukata na gaba dayan shekarar 2025 a watan Augusta kuma ba ta hanyar Man fetur ba>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, sun cimma yawan kudin shigar gaba dayan shekarar 2025 da ake bukata. Shugaban ya bayyana hakane a wajan wani taro inda yace kuma kudin ba ta bangaren man fetur suka zo ba. Yace kuma a yanzu Najeriya babu wani bankin cikin gida da yake binta bashi. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1962955483179839818?t=ZxXp8bt_-SseYE4CoIuhWA&s=19
Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai koma aiki nan da kwana 10 – Minista

Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai koma aiki nan da kwana 10 – Minista

Duk Labarai
Ministan sufurin Najeriya, Sa'idu Ahmed Alkali ya ce nan da kwana goma jirgin ƙasan Abuja-Kaduna da ya lalace zai koma aiki. A makon jiya ne dai jirgin ƙasan ya kauce hanya, inda ya tunsture a kusa da tashar Asham bayan ya taso daga Abuja zai tafi Kaduna ɗauke da mutum 618, ciki har da har da fasinja 583 da ma'aikatan jirgin ƙasan guda 15 da ma'aikacin jinya 1 da masu goge-goge 11, sannan aƙalla fasinja bakwai ne suka ji rauni. A wata ziyara da ministan sufurin ya kai wajen da jirgin ya kauce hanya a jiyar Litinin, ya yaba da ƙoƙarin jami'an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki bisa ƙoƙarin da suka yi wajen tabbatar da tsaron fasinjojin da sauran ma'aikatan jirgin har aka kwashe su. "A lokacin da jirgin ya tuntsure, jirgin yana tafiya ne da tarago guda bakwai. Tuni mun kwashe guda h...
Gwamnati ta bayyana jihohin arewacin Najeriya da za su iya fuskantar ambaliya a watan Satumba

Gwamnati ta bayyana jihohin arewacin Najeriya da za su iya fuskantar ambaliya a watan Satumba

Duk Labarai
Hukumar kula da madatsun ruwa ta Najeriya wato Nigeria Hydrological Services Agency (NiHSA) ta yi gargaɗin cewa aƙalla jihohin arewacin Najeriya guda 18 ne ke fuskantar barazanar ambaliya a mako biyu na farkon watan Satumban nan da aka shiga. A wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, ta ce jihohin Najeriya 29 ne tare da Babban Birnin Tarayya Abuja suke fuskantar barazanar ta ambaliya a tsakanin 1 zuwa 15 ga watan Satumba. Hukumar ta ce ambaliyar za ta iya shafar ƙananan hukumomi 107, da garuruwa 631, sannan aƙalla manyan titunan ƙasar 50 za su fuskanci tsaiko. Daga cikin jihohin da suka fi shiga barazanar, akwai Borno da Zamfara da Jigawa da Kebbi da Yobe da Filato da Gombe da Taraba da Sokoto, sannan akwai jihar Kaduna barazanar ba ta ƙarfi sosai.
Burkina Faso ta haramta auren jinsi

Burkina Faso ta haramta auren jinsi

Duk Labarai
Gwamnatin sojin Burkina Faso a ƙarƙashin jagorancin Faso Ibrahim Traore ta sanar da haramta auren jinsi a ƙasar baki ɗaya. Wannan na zuwa ne kimanin shekara guda bayan an amince da wani daftarin dokoki da aka yi garambawul a kan dokokin iyalin ƙasar, inda a ciki aka ƙara auren jinsi. Ƙasar da ke yankin Sahel ta kasance a cikin ƙasashen Afirka 22 a cikin 54 da suka amince da auren jinsi, lamarin da ke ɗaukar hukuncin kisa ko zaman gidan kaso mai tsaro a wasu ƙasashen. A jiya Litinin ne gwamnatin ƙasar ta amince da sabuwar dokar wadda ta haramta auren na jinsin. A sabuwar dokar, wanda aka kama da auren jinsi zai iya fuskantar zaman gidan yari na shekara biyar, kamar yadda ministan shari'a na ƙasar Edasso Rodrigue Bayala ya sanar a kafar gwamnatin ƙasar ta RTB. A bara ma dai ma...
Ban gaji Ko sisi daga mahaifina ba>>Inji Dangote

Ban gaji Ko sisi daga mahaifina ba>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa, bai gaji ko sisi daga hannun mahaifinsa ba. Ya bayyana hakane a wata tsohuwar hira da gidan jaridar Bloomberg suka yi dashi a shekarar 2020. Dangote yace bayan rasuwar mahaifinsa an bashi gadonsa amma sai ya kyautar da kudin, yace kuma yana alfahari da hakan. Sannan ya kara da cewa ya yiwa kawunsa aiki kadan inda daga baya ya bar Kano zuwa Legas inda ya fara sayar da sumunti Yace a wancan lokacin ana shigo da siminti ne cikin Najeriya.
Idan aka Tambayi dan tsigigi, Guntun Mugu, Wanene Ubangijinka a Kabari, zai ce Allah, idan aka tambayeshi Addininshi, zai ce Islam, amma ida aka Tambayeshi wanene shugabanka? Zai ce Buhari sai ya sha Guduma>>Inji Sheikh Zakzaky

Idan aka Tambayi dan tsigigi, Guntun Mugu, Wanene Ubangijinka a Kabari, zai ce Allah, idan aka tambayeshi Addininshi, zai ce Islam, amma ida aka Tambayeshi wanene shugabanka? Zai ce Buhari sai ya sha Guduma>>Inji Sheikh Zakzaky

Duk Labarai
Sheikh Zakzaky ya bayyana cewa, idan aka Tambayi dan tsigigi, Guntun Mugu a kabari wanene Ubangijinka, zai ce Allah, idan aka tambayeshi menene Addinin ka, zai ce Islam, sannan idan aka tambayeshi wanene shugabanka, zai ce Buhari. Yace daga nan ne za'a mai duka da guduma. Malam ya bayyana hakane a wani wa'azinsa da yayi. Duk da dai bai kira suna ba amma da yawa sun yi amannar cewa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yake. https://www.tiktok.com/@ansarmsh313/video/7545109236469091601?_t=ZS-8zOBAFRos88&_r=1
Kalli Bidiyon: Da An yi magana akan iyayen Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) sai ku ce cin mutunci ne toh idan dai hakan cin mutunci ne Allah da Qur’ani ne suja fara dan sun kai iyayen Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)wuUta>>Inji Sheikh Musa Asadussunnah

Kalli Bidiyon: Da An yi magana akan iyayen Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) sai ku ce cin mutunci ne toh idan dai hakan cin mutunci ne Allah da Qur’ani ne suja fara dan sun kai iyayen Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)wuUta>>Inji Sheikh Musa Asadussunnah

Duk Labarai
Malamin addinin Islama, Sheikh Musa Asadussunnah Sunnah ya bayyana cewa, da an yi magana akan iyayen Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) sai wasu su ce cin mutunci ne. Yace toh indai cin mutunci ne, to Qur'ani da Allah ne suka fara dan sun kai iyayen Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) din wuta. Malam ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi: https://www.tiktok.com/@gkbw3/video/7545222802664672519?_t=ZS-8zO8jUNhwR7&_r=1
Kalli Bidiyo: Waiku Wane irin mutanene shikenan mutum ba zai yi laifi ba ya tuba? Mu munsan Habu Damusa, Kuma tun kamin hawa mulkin El-Rufai ya tuba, Sheke mutane da yake da kwace a baya ne>>Inji Omar

Kalli Bidiyo: Waiku Wane irin mutanene shikenan mutum ba zai yi laifi ba ya tuba? Mu munsan Habu Damusa, Kuma tun kamin hawa mulkin El-Rufai ya tuba, Sheke mutane da yake da kwace a baya ne>>Inji Omar

Duk Labarai
Wani matashi me suna Omar ya bayyana cewa, Habu Dan Damisa, Watau dan dabar da yayi kaurin suna a Kaduna wanda ake zargin jami'an tsaro da kashewa ya tuba. Yace su sun san Malam Habu, yace tun kamin hawan mulkin El-Rufai ya daina kisa da kwace. Yace shekaru 3 da suka gabata babu wanda zai ce maka ya ga Habu yayi kisa ko kuma ya yi kwace. Yace shikenan kuma sai ace mutum ba zai yi laifi ya tubaba? https://www.tiktok.com/@umarsani830/video/7545158951990578453?_t=ZS-8zO6XCR8RUm&_r=1
Na fi Raba Gardama Ilimin Addini, Na fishi Zati na jaruman maza, yanda nake kamar dokin Ajantina>>Inji Sahir Abdul

Na fi Raba Gardama Ilimin Addini, Na fishi Zati na jaruman maza, yanda nake kamar dokin Ajantina>>Inji Sahir Abdul

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tauraron Kannywood, Sahir Abdul ya bayyana cewa, yafi abokin aikisa, Raba Gardama na Labarina Ilimin Addini da kuma zati na mazaje. Ya bayyana hakane a wata ganawa da aka yi dashi. Yace kaf Kannywood babu matashi kamarsa. https://www.tiktok.com/@mubarak_sarkawa/video/7545032658879892752?_t=ZS-8zO1l67H4ZV&_r=1