Wednesday, March 4
Shadow

Duk Labarai

Masu Laifi 16 sun tsere daga gidan gyara hali dake Keffi jihar Nasarawa

Masu Laifi 16 sun tsere daga gidan gyara hali dake Keffi jihar Nasarawa

Duk Labarai
Masu laifi 16 ne suka tsere daga gidan gyara hali na Keffi dake jihar Nasarawa Lamarin ya farune da sassafiyar ranar Talata. Me magana da yawun hukumar kula da gidajen gyara hali na kasa, Umar Abubakar ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace jami'an hukumar 5 ne suka jikkata sanadiyyar lamarin. Yace 2 daga ciki suna cikin mawuyacin hali Saidai yace an kama 7 daga cikin wadanda suka tsere kuma ana bin sahun sauran.
Amarya, Rahama Sadau ta godewa ‘yan Uwa da abokan arziki da suka tayata Biki

Amarya, Rahama Sadau ta godewa ‘yan Uwa da abokan arziki da suka tayata Biki

Duk Labarai
Tauraruwar Fina-finan Hausa, Rahama Sadau ta mika sakon godiya ga 'yan uwa da abokan arziki da suka tayata Biki. Rahama ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta inda tace bata da kalaman godiya da zata iya bayyana irin farin cikin da take ciki. "Ina mika sakon godiya ta musamman ga dangi, ’yan uwa da abokan arziki bisa fatan alheri da addu’o’in ku a game da Auren mu. Kalmominku da addu’arku sun karfafa mana guiwa kuma sun sa ranar ta kasance ta musamman. Allah Ya saka da alkhairi. Bani da kalmomin yi muku godia sai dai nace Allah ya saka muku da alheri, Allah yabar zumunchi na gode, na gode, Allah ya biyawa kowa bukatun sa na alheri. Ameen Ni kuma Allah ya bamu zaman lafia da Miji na Allah ya Albarkachi rayuwar auren mu. Ameen ya rabbil Alameen. Ina yiwa kowa fatan alhe...
Wasu magoya bayan Tinubu sun gaya min cewa ‘yan Arewa jahilaine>>Inji Babachir Lawal

Wasu magoya bayan Tinubu sun gaya min cewa ‘yan Arewa jahilaine>>Inji Babachir Lawal

Duk Labarai
Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal ya bayyana cewa, Akwai wata kungiyar magoya bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da yake cikinta wadda suka ce 'yan Arewa jahilaine. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace ya gaya musu cewa wannan mutane sune ake neman kuri'arsu. Yace Salon Mulkin Tinubu bai yi masa ba inda yace da ace yana cikin gwamnatin Tinubu da tuni ko dai ya sauka daga mukaminsa ko an koreshi ko wani abun.
Kalli Bidiyo: Falalar Salatil Fatih itace idan ka karantashi zaka samu ladar sauke Qur’ani daga Dubu 1 abinda yayi sama>>Inji Sheikh Abdulfatahi Sani

Kalli Bidiyo: Falalar Salatil Fatih itace idan ka karantashi zaka samu ladar sauke Qur’ani daga Dubu 1 abinda yayi sama>>Inji Sheikh Abdulfatahi Sani

Duk Labarai
Malamin darikar Tinjaniyya, Sheikh Abdulfatahi Sani ya bayyana cewa, Salatul Fatih bai fi Qur'ani ba. Yace amma ana maganar lada ne. Yace Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya gayawa shehu duk wanda ya karanta Salatil Fatih zai sau ladar sauke Qur'ani sau 1000 zuwa sama. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi. https://www.tiktok.com/@zubairuabdullahi77/video/7536898346557000965?_t=ZS-8yoKXxpimIr&_r=1
Jam’iyyar ADC ta kadu yayin da EFCC ta fara farautar ‘yan jam’iyyar, Yanzu haka EFCC ta gayyaci tsaffin Gwamnoni 3 na jam’iyyar

Jam’iyyar ADC ta kadu yayin da EFCC ta fara farautar ‘yan jam’iyyar, Yanzu haka EFCC ta gayyaci tsaffin Gwamnoni 3 na jam’iyyar

Duk Labarai
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC ta gayyaci tsaffin Gwamnoni 3 na jam'iyyar ADC. Hakan ya saka rudani a jam'iyyar ta ADC inda sukw zargin kokarin murkushe su ne yasa EFCC ta fara bincken membobin jam'iyyar. Tuni dai EFCC ta kama tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal inda take tuhumarsa bisa cire wasu kudi da suka kai Naira Biliyan 189 lokacin yana gwamnan Sokoto. Me magana da yawun jam'iyyar ADC, Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa, wannan abu ana kokarin ganin an tursasa mutane sun bar jam'iyyar ta ADC ne. Inda ya tabbatarwa da jaridar Punchng cewa an gayyaci tsaffin gwamnoni 3 zuwa EFCC amma yace ba zai fadi sunayensu ba.
Kalli Bidiyon Haduwar G-Fresh da Sheikh Ibrahim Maqari inda yace ya ji wa’azin da malam ya masa kuma yanzu zai rika fadakarwa ko da ta hanyar wasa ne

Kalli Bidiyon Haduwar G-Fresh da Sheikh Ibrahim Maqari inda yace ya ji wa’azin da malam ya masa kuma yanzu zai rika fadakarwa ko da ta hanyar wasa ne

Duk Labarai
A karshe dai Tauraron Tiktok, GFRESH Al-amin ya hadu da Sheikh Ibrahim Maqari inda yace ya ji nasihar da malam ya masa. Gfresh yace zai rika fadakarwa yanzu ko da ta hanyar wasa ne. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7536960885865073926?_t=ZS-8yoDr9ou5Wz&_r=1 A jiya ne dai aka ga Gfresh a gaban malam yana tambayar shin ko ya halatta mutum ya rika Bidiyo da iyalinsa yana watsawa Duniya. Malam dai ya bashi Amsar cewa, idan abinda ake yi bai sabawa addini ba, babu matsala.
Gwamnatin tarayya na barzanar korar ma’aikata, 3,598 daga aiki

Gwamnatin tarayya na barzanar korar ma’aikata, 3,598 daga aiki

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya na barazanar korar ma'aikata, 3,598 da suka ki yin tantancewa daga aiki. Gwamnatin tace idan aka sake yin tantancewar, duk wanda bai yadda an tantanceshi ba, za'a dauka kawai takardat daukar aiki ta boge gareshi. Za'a yi tantancewarce daga ranar 18 ga watan Augusta zuwa ranar 28 ga watan a ma'aikatu daban-daban na tarayya. An bukaci ma'aikatan dasu gabatar da takardun daukarsu aiki dana karin girma da sauransu.
Kamun da akawa Tsohon Gwamnan Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal siyasa ce kawai>>Inji PDP

Kamun da akawa Tsohon Gwamnan Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal siyasa ce kawai>>Inji PDP

Duk Labarai
Jam'iyyar PDP, Reshen jihar Sokoto ta bayyana cewa, kamun da akawa tsohin Gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal siyasa ce. Me magana da yawun jam'iyyar, Hassan Sanyinnawal ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai da safiyar ranar Talata. Yace EFCC ta bar asalin masu rashawa da cin hanci inda take kama irin su Tambuwal. Yace hakan kokari ne na dakile 'yan Adawa da kuma hana yiwa shugaba Tinubu suka da gaya mai gaskiya. Ya yi kira ga masoyan Tambuwal su kwantar da hankali amma su tsaya kai da kafa wajan goyon bayansa.
Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Maraba Da Naɗin Maryam Bukar Hassan A Matsayin Jakadiyar Zaman Lafiya Ta Duniya

Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Maraba Da Naɗin Maryam Bukar Hassan A Matsayin Jakadiyar Zaman Lafiya Ta Duniya

Duk Labarai
Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Maraba Da Naɗin Maryam Bukar Hassan A Matsayin Jakadiyar Zaman Lafiya Ta Duniya. A yau Litinin ne gwamnatin shugaba Tinubu ta karɓi baƙuncin fitacciyar mai waƙar baka Maryam Hasan wadda ta yi nasarar zama jakadiyar zaman lafiya ta majalisar dinkin duniya. Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ne ya karbi bakuncin jakadiyar da tawagarta a fadar shugaban ƙasa inda ya bayyana farincikin gwamnati da shirinta na yin aiki da jakadiyar yar asalin Najeriya don ƙarfafa zaman lafiya a Najeriya da ma duniya baki ɗaya. Da yake jawabi ga tawagar ta Global Advocate for Peace ta Majalisar Dinkin Duniya, Shettima ya bayyana Maryam a matsayin mace mai tsayuwar daka wajen sadaukar da basirarta ga wanzar da zaman lafiya musamman a wata ƙasidarta mai taken 'Rikici bai...