Wednesday, March 4
Shadow

Duk Labarai

Umar Bazaza ya nemi a bashi auren dalibai mata da suka ciwo gasar Turanci ta Duniya

Umar Bazaza ya nemi a bashi auren dalibai mata da suka ciwo gasar Turanci ta Duniya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Ina mai baiyana farin cikina na ganin 'yan iwanmu mata, kannen mu kuma 'yan kasar mu Nijeriya, kuma 'yan jihata ta Yobe daya kuma 'yar garina na Poatiskum samum damar lashe gasar Turanci ta duniya. Tabbas Babu Abunda za mu cewa Allah sai godiya zaboda ba karamar nasara bane samun Irin wannan a kasar musanman jiharka kma garinka. Muna rokon Allah Ya jikan wanda ya assasa wannan makarantar wato marigayi Gwamna Mamman Bello. Wanda dalilin makarantar har 'yan uwanmu suka samu ilmin d...
A Karshe Dai Mutumin Da Ya Yi Tattaki Daga Jigawa Zuwa Kano Domin Ganin Gwamna Abba Kabir Ya Isa Kofar Fadar Gwamnatin Kano, Inda Ya Ce Ko Zai Yi Shekara Guda Ba Zai Tafi Ba Har Sai Ya Ga Abba

A Karshe Dai Mutumin Da Ya Yi Tattaki Daga Jigawa Zuwa Kano Domin Ganin Gwamna Abba Kabir Ya Isa Kofar Fadar Gwamnatin Kano, Inda Ya Ce Ko Zai Yi Shekara Guda Ba Zai Tafi Ba Har Sai Ya Ga Abba

Duk Labarai
A Karshe Dai Mutumin Da Ya Yi Tattaki Daga Jigawa Zuwa Kano Domin Ganin Gwamna Abba Kabir Ya Isa Kofar Fadar Gwamnatin Kano, Inda Ya Ce Ko Zai Yi Shekara Guda Ba Zai Tafi Ba Har Sai Ya Ga Abba A lokacin da yake hanyar tahowa dai, gwamnatin Kano ta bakin kakakin Gwamna Abba ya umarci mutumin da ya koma gida amma duk da haka ya bijire ya taho. Me za ku ce?
Sabuwar Baraka ta kunno kai a jam’iyyar ADC, Ana zargin Atiku da saye duk wani me fada aji a jam’iyyar da kudi, Peter Obi ya koka da cewa an mayar dashi saniyar ware

Sabuwar Baraka ta kunno kai a jam’iyyar ADC, Ana zargin Atiku da saye duk wani me fada aji a jam’iyyar da kudi, Peter Obi ya koka da cewa an mayar dashi saniyar ware

Duk Labarai
Rahotanni daga jam'iyyar ADC na cewa ana zargin Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar da saye duk wani me fada a ji a jam'iyyar da kudi. Rahoton na jaridar Punchng yace duk sun koma abinda Atiku yake so shi ake yi a jam'iyyar. Wasu masana harkar jam'iyyar ne suka sanar da jaridar wannan batu amma sun ce kada a fadi sunayensu dan kada a hukutasu. Saidai me magana da yawun jam'iyyar ta ADC, Bolaji Abdullahi ya musanta wannan zargi inda yace za'awa kowa adalci a jam'iyyar. Kuma abinda ke gabansu a yanzu shine kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zabe a shekarar 2027. Hakan na zuwane bayan da shugaban magoya bayan Peter Obi, Tanko Yunusa ya koka da cewa ba'a yi dasu an mayar dasu saniyar ware a jam'iyyar ADC. A baya dai an rika rade-radin cewa, Peter O...
Kalli Bidiyon yanda Garzali Miko ya manta ya bar Data a kunne yana bacci a yayin da yake tsaka da yin Live a Tiktok

Kalli Bidiyon yanda Garzali Miko ya manta ya bar Data a kunne yana bacci a yayin da yake tsaka da yin Live a Tiktok

Duk Labarai
Bidiyo ya bayyana inda aka ji cewa, Tauraron fina-finan Hausa, Kuma Mawaki, Garzali Miko ya manta ya bar datarsa a bude bacci ya kwasheshi yayin da yake Live a Tiktok. An dai ji shi yana ta munshari a Bidiyon. Zuwa yanzu dai Garzali bai tabbatar ko karyata wannan Bidiyon ba ko kuma bayar da karin bayani kan lamarin ba. https://www.tiktok.com/@binsadeeq02/video/7535612288393383190?_t=ZS-8yhOuTTN7EO&_r=1
Akwai matsala a sakamakon da muka saki, WAEC tace dalibai su sake duba sakamakon jarabawarsu a yau

Akwai matsala a sakamakon da muka saki, WAEC tace dalibai su sake duba sakamakon jarabawarsu a yau

Duk Labarai
Hukumar shirya jarabawar kammala Sakandare ta WAEC ta bayyana cewa, akwai tangarda a sakamakon data saki a farko. Dan haka ne ta dakatar da duba sakamakon inda tace a ranar Juma'a dalibai su sake duba sakamakon jarabawarsu. Hukumar ta sanar da hakanne ta bakin me kula da hulda da jama'ar ta, Moyosola Adesina. Bayan sakin sakamakon farko, an samu korafi daga iyaye ka yawan faduwar da aka yi jarabawar ta bana inda har wasu ke kiran a soke jarabawar ta bana.
Kashi 60 na abinci a Najeriya na lalacewa saboda rashin wuraren adana – NAFDAC

Kashi 60 na abinci a Najeriya na lalacewa saboda rashin wuraren adana – NAFDAC

Duk Labarai
Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC), ta ce kashi 60 na abinci a Najeriya na lalacewa ne sakamakon rashin wuraren adana abinci da suka dace. Darakta-janar na NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye ce ta bayyana haka a cikin shirin Sunrise Daily na gidan talabijin na Channels, inda ta ce wuraren adana abinci sun yi kaɗan a ƙasar. Ta ce idan aka samu wuraren adana abinci masu kyau, dangin abinci irin ganyayyaki da su tumatiri duka ba za su ci gaba da lalacewa ba. Ta ce hakan ne ya sa suke ɗuakar matakai na ganin abinci da ake adanawa sun ɗauki lokaci ba su lalace ba ta hanyar samar da wuraren adana na zamani.
Atiku ya bukaci a saki Sowore

Atiku ya bukaci a saki Sowore

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi Alla-wadai da kamawa tare da tsare fitaccen ɗan gwagwarmayar, Omoyele Sowore. Atiku ya ce abin kunya ne cin zarafi da tawagar sa ido na sufeto janar na ƴansandanƙasar suka yi wa Sowore. "Bai dace a tsare Sowore ba, kuma hakan ba ya cikin ka'ida. Dole ne a yi tur da batun," in ji Atiku. Ya ce laifin ɗan gwagwarmayar kawai shi ne don ya fito ya yi magana kan rashin adalci da kuma kyayyawar shugabanci da ake yi a Nijeriya. Wasu rahotanni ma na bayyana cewa an lakaɗawa Sowore duka har ma ƙarya masa hannu, inda ake zargin ƴansanda da aikatawa. Wazirin na Adamawa ya ce wannan abin da ƴansanda suka aikata ba ga Sowore kaɗai bane, inda ya ce hakan ya nuna cewa za a far wa kowane ɗan Najeriya da ya yi ƙoƙarin fitowa ya faɗi ga...
An kayyade naira miliyan 8.5 kafin alkalami na kuɗin aikin Hajjin 2026

An kayyade naira miliyan 8.5 kafin alkalami na kuɗin aikin Hajjin 2026

Duk Labarai
Hukumar kula da aikin Hajji ta Najeriya NAHCON, ta bayyana cewa an kayyade naira miliyan 8.5 a matsayin kafin alkalami na kuɗin aikin Hajjin 2026. NAHCON ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Alhamis, bayan gudanar da taro da shugabanni da kuma sakatarorin hukumomin aikin hajji na jihohin ƙasar - don fara fara shirye-shiryen ibadar ta wannan shekarar ta Musulunci. Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ce an kayyade miliyan 8.5 ɗin ne a matsayin kafin alkalami na aikin hajjin baɗi, kafin a kammala tattaunawa don sanin haƙikanin kuɗin. Ya ce Saudiyya ta sake bai wa Najeriya gurbin kujeru 95,000, kamar yanda ta samu a bara. Farfesa Usman ya kuma yaba wa shugaba Bola Tinubu bisa irin goyon baya da yake bai wa hukumar da kuma alhazan Najeriya - inda...
Sam babu Adalci: Soja ya soki shugaba Tinubu saboda baiwa ‘yan kwallo kyautar Naira Miliyan 50 inda ya nuna dakunan bukka da suke kwana a ciki a daji

Sam babu Adalci: Soja ya soki shugaba Tinubu saboda baiwa ‘yan kwallo kyautar Naira Miliyan 50 inda ya nuna dakunan bukka da suke kwana a ciki a daji

Duk Labarai
Sojan Najeriya ya koka da rashin adalci bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa 'yan kwallo mata kyautar Naira Miliyan 150. Sojan yace albashinsu dubu dari ne inda ya nuna dakunan bukka da suke kwana yace sam babu adalci a lamarin. https://twitter.com/oxygist/status/1953465690469335432?t=m-z8alJwI3WyQpQeoP7o4w&s=19