Tuesday, December 16
Shadow

Duk Labarai

Jihar Jigawa ta dakatar da Albashin malaman makarantar Firamare 239 da aka samu basa zuwa aiki, ciki hadda wanda ya shekara 3 bai je wajan aikin ba

Jihar Jigawa ta dakatar da Albashin malaman makarantar Firamare 239 da aka samu basa zuwa aiki, ciki hadda wanda ya shekara 3 bai je wajan aikin ba

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Jigawa na cewa, Hukumar Ilimin bai daya UBE ta jihar ta dakate da albashin malaman makarantar Firamae 239 da aka samu da laifin rashin shiga aiki su koyar da dalibai ko rashin zuwa wajan aiki. Shugaban hukumar, Prof. Haruna Musa ya bayyana cewa wannan kokari ne na tsaftace aikin gwamnati. Sannan yayi kira ga al'umma da su rika lura su kai karar wadanda basa zuwa wajan aikin. Daga cikin wadanda aka dakatar da albashin nasu akwai malamin da ya shekara 3 kanan bai je wajan aikin ba
Kamfanin DSTV da sauran tashoshi na Tauraron dan Adam sun tafka asarar Dala Miliyan $158.19 saboda ‘yan Najeriya da yawa yanzu sun daina saka kati saboda matsin tattalin arziki

Kamfanin DSTV da sauran tashoshi na Tauraron dan Adam sun tafka asarar Dala Miliyan $158.19 saboda ‘yan Najeriya da yawa yanzu sun daina saka kati saboda matsin tattalin arziki

Duk Labarai
Rahotanni sun ce Kamfanin Multichoice wanda su DSTV suke karkashin sa sun tafka mummunar asara saboda 'yan Najeriya da yawa sun daina saka kati suna kallon tashoshin. Kudin shigar kamfanin a shekarar data gabata yayi kasa da kaso 44 cikin 100 inda a yanzu suka samu kudin shiga da ya kai dala Miliyan $197.74. Saidai a shekarun baya suna samun kudin shiga da ya kai dala Miliyan $355.93. Hakan na nufin sun tafka asarar dala Miliyan $158.19 idan aka kwatanta da shekarar data gabata. Lamarin dai bai zowa mutane da mamaki ba musamman ganin yanda kasar ke cikin hali na matsin tattalin arziki. Hakan kuma baya rasa nasaba da karin kudin subscription da DSTV din suka yi daga Naira N29,500 zuwa Naira 37,000 duk wata.
Ina Goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027 ido rufe, saboda babu shugaban da ya taba yin abinda yayi>>Inji Gwamnan Jihar Gobe, Inuwa Yahya

Ina Goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027 ido rufe, saboda babu shugaban da ya taba yin abinda yayi>>Inji Gwamnan Jihar Gobe, Inuwa Yahya

Duk Labarai
Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahya yace zai yi aiki tukuru dan goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zarce a shekarar 2027. Gwamnan ya bayyana hakane a yayin kaddamar da wani shirin noma da kiwo a jiharsa. Gwamnan yace Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya warew shirin Naira Biliyan 120 dan karfafa kiwo kuma ya amince a bayar da kaso 50 cikin 100 na kudin. Yace babu shugaban Arewa da aka yi a baya da ya taba warewa bangaren kiwo irin wadannan makuda kudade duk da cewa yankin Arewa an sanshi da kiwo. Yace bisa haka suna goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zarce. Yace zasu goyi bayanshi ido Rufe dan ya sake zama shugaban kasa a 2027. “I assure the President that for what he has done, is doing, and will do, Gombe people will follow him to the battlefield bl...
Manyan Ma’aikatan mu ne ke ta tafiya lahira akai-akai babu kakkautawa shiyasa muka ce a yi Azumi ko zamu samu sauki>>Ma’aikatar Noman Najeriya

Manyan Ma’aikatan mu ne ke ta tafiya lahira akai-akai babu kakkautawa shiyasa muka ce a yi Azumi ko zamu samu sauki>>Ma’aikatar Noman Najeriya

Duk Labarai
Shiga tasharmu ta WhatsApp dan samun labarai: https://whatsapp.com/channel/0029VbA9rBN1SWt61nQZUj1g Ma'aikatar noma ta Najeriya ta bayyana cewa manyan ma'aikatan hukumar ne ke ta mutuwa shiyasa ma'aikatar ta fito da tsarin yin Azumin dan neman taimakon Allah. Hakan na zuwane bayan da aka samu rahotanni dake cewa, ma'aikatar ta nemi ma'aikatan ta da su dauki azumi dan neman nasarar wadatar Abinci a Najeriya. Saidai a sanarwar da mataimakiyar me yada labarai ta hukumar, Ezeaja Ikemefuna ta fitar tace zancen ba haka yake ba. Tace manyan ma'aikatan hukumar ne ke ta mutuwa akai-akai shiyasa suka fito da tsarin yin addu'a ta hanyar Azumi dan neman sauki da daukin Allah. Saidai Tuni an dakatar da yin azumin wanda da za'a fara ranar Litinin bayan da cece-kuce yayi yawa akan Lamarin...
Bankin Duniya ya bayar da tallafin Dala Miliyan $40 a rabawa talakawan Najeriya

Bankin Duniya ya bayar da tallafin Dala Miliyan $40 a rabawa talakawan Najeriya

Duk Labarai
Shiga tasharmu ta WhatsApp dan samun labarai: https://whatsapp.com/channel/0029VbA9rBN1SWt61nQZUj1g Bankin Duniya ya ware dala Miliyan $40 dan tallafi ga talakawa mafiya rauni a Najeriya. Tun a watan Satumba na shekarar data gabata ne dai Bankin ya amince da bayar da wadannan kudade a matsayin bashi amma sai yanzu za'a bayar dasu. Tallafin za'a bayar dashi ne da karfafa 'yan Najeriya da yawa kuma zai ci gaba har nan da zuwa shekara 2029
Hedikwatar Tsaro ta Nijeriya ta tabbatar da kama wani ɗan kasar China bisa zargin taimaka wa ƴan ta’adda

Hedikwatar Tsaro ta Nijeriya ta tabbatar da kama wani ɗan kasar China bisa zargin taimaka wa ƴan ta’adda

Duk Labarai
Hedikwatar Tsaro ta Nijeriya ta tabbatar da kama wani ɗan kasar China bisa zargin taimaka wa ƴan ta’adda. Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta tabbatar da kama wani ɗan ƙasar China yayin wani samamen yaƙi da ta’addanci da aka gudanar a Jihar Borno. Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Tsaro, Manjo- Markus Kangye, ne ya tabbatar da hakan a madaJanardin manyan hafsoshin soji a ranar Juma’a. Sai dai Manjo-Janar Kangye bai bayyana sunan baƙon ba, amma ya ce mutumin da ya bayyana kansa a matsayin mai hakar ma’adanai yana hannun dakarun soji yanzu kuma ana ci gaba da bincikarsa. Kama ɗan ƙasar China ɗin ya faru ne kasa da mako guda bayan rundunar soji ta bayyana kama wasu 'yan Pakistan huɗu da ake zargin suna koyar da 'yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas. Yayin da ake tambayarsa ...
Da Duminsu: Shugaban kasar Amurka Donald Trump zai haramtawa ‘yan Najeriya shiga Amurka

Da Duminsu: Shugaban kasar Amurka Donald Trump zai haramtawa ‘yan Najeriya shiga Amurka

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka Donald Trump na shirin dakatar da karin kasashe 36 daga shiga kasar Amurkar kuma ana tsammanin Najeriya ka iya shiga ciki. A cikin kasashen da Trump din ke shirin dakatarwa akwai kasashen Afrika guda 25 ciki hadda kasar Egypt da Djibouti sannan akwai kasashen Asia. Kafar the Washington post ta kasar Amurkar tace ta yi kokarin jin ta bakin fadar White House amma abu ya ci tura.
Idan Ana son yin sulhu da mu sai an daina kiran mu da sunan ‘yan ta’adda>>Inji Aliero

Idan Ana son yin sulhu da mu sai an daina kiran mu da sunan ‘yan ta’adda>>Inji Aliero

Duk Labarai
Babban dan Bindiga, Ado Aliero yace shi da yaransa ba zasu daina kai hare-hare da yin garkuwa da mutane ba sai an daina kiransu da sunan 'yan ta'adda. Zagazola Makama ya ruwaito cewa, Aliero ya fadi hakane a Dan Musa jihar Katsina yayin da aka yi zaman Sulhu dasu. Sarakunan gargajiya, Jami'an tsaro da shuwagabannin kananan hukumomi da 'yan Bindigar ne suka halarci wannan zaman na sulhu. Yace da yawan matasa da suka shiga harkar garkuwa da mutane matsin rayuwa nw ya jefasu cikin harkar. Yace iyayensu basa farin ciki da irin wannan rayuwar da suke yace ko da su kansu a zuciyarsu ba son irin wannan rayuwar suke ba, sun fi so a koma girmama juna musamman tsakaninsu da manoma. Yace dan haka kamin ma a fara maganar sulhu sai kowane sashe ya girmama dayan sashen.
Ƴansanda sun kuɓutar da mutum 73 da aka yi garkuwa da su a Katsina

Ƴansanda sun kuɓutar da mutum 73 da aka yi garkuwa da su a Katsina

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan jihar Katsina ta ce ta ceto mutum 73 da aka yi garkuwa da su. Ta kuma ce ta kama mutum 75 waɗanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar. Wata sanarwa da mai magana da yawun ƴansandan jihar, Abubakar Sadiq ya fitar, ta ce ana zargin mutum 15 cikin mutanen da laifin fashi da makamai, yayin da wasu 20 kuma da laifin kisa. "An kama mutum guda da laifin mallakar bindiga, 30 da zargin aikata fyaɗe sannan 108 kuma an kama su ne da wasu laifukan," in ji sanarwar. Sadiq ya ce makaman da aka ƙwato daga wajen mutanen sun haɗa da bindigar AK-49, karamar bindiga ƙirar pistol, ɗaruruwan harsasai, babura biyu da kuma shanu 174 da ake zargin sun sace. Ya ce ana ci gaba da kula da waɗanda aka kuɓutar daga hannun masu garkuwan.