Saturday, February 14
Shadow

Duk Labarai

Amaechi ya bayyana hanya daya da ADC zata bi ta iya kayar da Tinubu a zaben 2027

Amaechi ya bayyana hanya daya da ADC zata bi ta iya kayar da Tinubu a zaben 2027

Duk Labarai
Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya bayyana cewa, hanya daya da ADC zata kayar da APC a zaben 2027 shine ta tsayar da dan takarar shugaban kasa daga kudu. Ya bayyana cewa, Karfin Tinubu a Kudu ne, idan aka samu dan takara daga kudu, zai raba kuri'ar kudun. Dan haka sai a bar Arewa ta yanke shawarar wanda zai zama shugaban kasa. https://twitter.com/i/status/2011329217963966963
Kalli Bidiyon: Murja Kunya na gayawa Adam A. Cewa ya fito takarar Gwamna

Kalli Bidiyon: Murja Kunya na gayawa Adam A. Cewa ya fito takarar Gwamna

Duk Labarai
An hango Tauraruwar Tiktok, Murja Kunya na gayawa Adam A. Zango cewa, ya fito takarar gwamna zasu goyi bayansa. Murja Kunya ta bayyana hakane a yayin da suka hadu da Zango a wajan wani taron Biki. https://www.tiktok.com/@og_adam_a_zango_official/video/7594999270588075285?_t=ZS-933nxCO3BiK&_r=1 An Kuma Ganta suna waka tare da Adamun. https://www.tiktok.com/@og_adam_a_zango_official/video/7594987229353741588?_r=1&_t=ZS-933otP3wqXp
Kwankwaso yayi karin haske kan Rahoton cewa ya amincewa Abba ya koma jam’iyyar APC

Kwankwaso yayi karin haske kan Rahoton cewa ya amincewa Abba ya koma jam’iyyar APC

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya amincewa Abba Kabir Yusuf ya koma jam'iyyar APC. Saidai a wata sabuwar sanarwa daga Jam'iyyar NNPP ta karyata wannan Rahotan wanda kafar Premium times ta ruwaito. Sakataren jam'iyyar ta NNPP, Ladipo Johnson ya bayyana cewa, cewa wannan rahotan ba gaskiya bane. Yace wanda zasu koma jam'iyyar APC su koma amma su daina yaudarar Talakawa da cewa, wai Kwankwaso ya amince musu.
Ji yanda jami’an tsaro suka kama abubuwan fashewa a garin Daura dake jihar Katsina

Ji yanda jami’an tsaro suka kama abubuwan fashewa a garin Daura dake jihar Katsina

Duk Labarai
Rahotanni daga garin Daura na jihar Katsina sun bayyana cewa, hukumomi sun kama wata motar Golf dauke da ababen fashewa. Lamarin ya farune ranar 7 ga watan Janairu. Kakakin 'yansandan jihar, DSP Abubakar Aliyu ya tabbatar da hakan inda yace sun kama Direban motar me suna Jamilu Musa dan shekaru 40. Yace an bashi kayan ne daga Kano zuwa Kongolom. Bayan da bincike ya tsananta, an sake kama karin wasu mutane 2, Ibrahim Murtala da Sulaiman Muhammad. Hukumomin 'yansandan sun bayyana cewa, za'a gurfanar dasu a gaban kotu.
Gwamnatin tarayya ta dauki wasu Amurkawa aiki dan su rika tabbatarwa da Gwamnatin Amurka cewa tana baiwa Kiristoci kariya

Gwamnatin tarayya ta dauki wasu Amurkawa aiki dan su rika tabbatarwa da Gwamnatin Amurka cewa tana baiwa Kiristoci kariya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta dauki wasu Amurkawa aiki inda zata biyasu dala Miliyan $9 dan su rika gayawa Gwamnatin kasar Amurkar kokarin da suke yi na baiwa Kiristocin Najeriya kariya. Kafar TheCable tace sunan kamfanin Amurkar da zaiwa Gwamnatin Najeriya aiki DCI Group, shi wannan kamfanin aikinsa shine ya rika taimakawa duk wani me son yin hulda da kasar ta Amurka kaiwa Gwamnatin bayani. Dan hakane Gwamnatin tarayya ta daukeshi aiki ya rika kaiwa Gwamnatin tarayya bayanai kan kokarin da take na baiwa Kiristocin Najeriya kariya. Hakan na zuwane yayin sa kasar Amurka ta zargi Gwamnatin Najeriya da cewa, tana bari ana Mhuzghunawa Kiristoci a Najeriya.