Sunday, February 15
Shadow

Duk Labarai

Bayan da Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya baiwa Adam A. Zango mota, Shima Musa Mai Sana’a yace yana mika kokon bararsa wajan Kashim

Bayan da Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya baiwa Adam A. Zango mota, Shima Musa Mai Sana’a yace yana mika kokon bararsa wajan Kashim

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a ya bayyana cewa yana mika kokensa ga mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima akan cewa ya yiwa APC wahala amma har yanzu ba'a bashi komai ba. Ya bayyana cewa, dashi aka yi yakin neman zabe da komai amma ko sannu babu wanda yace masa. Dan haka yace yasan mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima mutum me me tausai shiyasa yake mika kokon bararsa a wajansa. https://www.tiktok.com/@maisanaakanotv/video/7592337982741368120?_t=ZS-930mxOR4nb6&_r=1 Ya bayyana hakane bayan da Mataimakin shugaban kasar ya baiwa abokin aikinsa, Adam A. Zango kyautar mota ta Naira Miliyan 80.
Kalli Bidiyon: Abin Kunyar da ‘yan Kungiyar Barcelona suka yi bayan sun lashe kofi da ake ta magana akai

Kalli Bidiyon: Abin Kunyar da ‘yan Kungiyar Barcelona suka yi bayan sun lashe kofi da ake ta magana akai

Duk Labarai
Bayan nasarar da Barcelona ta samu Akan Real Madrid inda aka ga taci Real Madrid 3-2 a daren jiya. A yayin da suke Murna, An ga Lamine Yamal yana Live a Instagram. Saidai an hango golan Barcelona, Wojciech Szczęsny yana zukar Tàbà. Nan da nan, Lamine Yamal ya dakatar da live din da yake yi. Lamarin ya jawo cece-kuce sosai. https://twitter.com/i/status/2010641777561362930
YANZU-YANZU: An Baza Jami’an Tsaro A Fadar Gwamnatin Kano, Biyo Bayan Rade-Radin Shirin Komawar Gwamna Abba Da Mukarrabansa Jam’iyyar APC A Yau Litinin

YANZU-YANZU: An Baza Jami’an Tsaro A Fadar Gwamnatin Kano, Biyo Bayan Rade-Radin Shirin Komawar Gwamna Abba Da Mukarrabansa Jam’iyyar APC A Yau Litinin

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kano sun bayyana cewa, an baza jami'an tsaro a yayin da ake shirin komawar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf jam'iyyar APC. A yau 12 ga watan Janairu ne dai ake tsammanin Gwamna Abba zai koma jam'iyyar APC. Tuni tsohon shugaban jam'iyyar kuma tsohon gwamnan jihar ta Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya koma Kanon daga Dubai dan halartar wannan taron.
Kasar Algeria ta shigar da kara akan Rafalin da ya hura wasanta da Najeriya

Kasar Algeria ta shigar da kara akan Rafalin da ya hura wasanta da Najeriya

Duk Labarai
Kasar Algeria ta shigar da Rafalin da ya hura wasan ta da Najeriya dan kasar Senegal me suna, Issa Sy kara. Hakanan a yanzu tana son kara shigar da Rafalin kara a karo na biyu. Hukumar kwallon kafa ta Algeria, FAF ce ta sanar da hakan inda suke zargin Rafalin da rashin Adalci. Sun yi zargin cewa sun samu Penalty ya hana hakanan kuma bayan wasan ya gaisa da 'yan wasan Najeriya amma bai gaisa da 'yan wasan Algerian ba. Hakanan kuma sun zargi cewa bayan an kammala wasan an co zarafinsu. Wasan dai ya tashi Najeriya na cinsu 2-0.
Shugaban karamar hukuma a jihar Jigawa ya bayyana cewa a yanzu suna samun kudin su kai tsaye daga gwamnatin tarayya

Shugaban karamar hukuma a jihar Jigawa ya bayyana cewa a yanzu suna samun kudin su kai tsaye daga gwamnatin tarayya

Duk Labarai
Wani shugaban karamar hukuma a jihar Jigawa ya bayyana cewa, a yanzu suna samun kudin shigarsu kai tsaye daga gwamnatin tarayya. Ya bayyana hakane bayan gargadin da shugaba Tinubu yawa gwamnoni cewa a daina yin katsalandan a kudaden kananan hukumomi a rika basu kudadensu kai tsaye. Wannan na tabbatar da cewa, an ji gargadin na shugaba Tinubu.