Ba matsala bane dan siyasar Najeriya ta koma Jam’iyya daya kawai, Adalcin Shugaba Tinubu ne yake kawo ‘yan siyasa APC>>Inji Ganduje
Shugaban jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya ce samun jam'iyyu barkatai na dagula tafiyar da gwamnnati a tsarin dimokraɗiyya.
Abdullahi Ganduje ya shaida hakan ne bayan ganawa da Shugaba Tinubu tare da wasu ƴan majalisar PDP da suka koma APC.
Shugaban, ya ce idan duka jam'iyyun siyasar ƙasar za su narke su koma APC, suna maraba da hakan.
''Yanzu idan ka duba ƙasar China tsarin jam'iyya guda suke bi, amma yau ƙasar China jagora ce a duniya wajen samar da ci gaban al'ummarsu''.
Ganduje ya ce idan ƴan Najeriya suka buƙaci komawa tsarin jam'iyyar guda, ba wanda zai yi faɗa da hakan.
Ƴanmajalisar Dattawan Najeriya uku na babbar jam'iyyar hamayya ta PDP daga jihar Kebbi za su sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC mai mulki, kamar yadda shugaban jam'iyyar APC na ƙ...








