Monday, May 4
Shadow

Duk Labarai

Ba matsala bane dan siyasar Najeriya ta koma Jam’iyya daya kawai, Adalcin Shugaba Tinubu ne yake kawo ‘yan siyasa APC>>Inji Ganduje

Ba matsala bane dan siyasar Najeriya ta koma Jam’iyya daya kawai, Adalcin Shugaba Tinubu ne yake kawo ‘yan siyasa APC>>Inji Ganduje

Duk Labarai
Shugaban jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya ce samun jam'iyyu barkatai na dagula tafiyar da gwamnnati a tsarin dimokraɗiyya. Abdullahi Ganduje ya shaida hakan ne bayan ganawa da Shugaba Tinubu tare da wasu ƴan majalisar PDP da suka koma APC. Shugaban, ya ce idan duka jam'iyyun siyasar ƙasar za su narke su koma APC, suna maraba da hakan. ''Yanzu idan ka duba ƙasar China tsarin jam'iyya guda suke bi, amma yau ƙasar China jagora ce a duniya wajen samar da ci gaban al'ummarsu''. Ganduje ya ce idan ƴan Najeriya suka buƙaci komawa tsarin jam'iyyar guda, ba wanda zai yi faɗa da hakan. Ƴanmajalisar Dattawan Najeriya uku na babbar jam'iyyar hamayya ta PDP daga jihar Kebbi za su sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC mai mulki, kamar yadda shugaban jam'iyyar APC na ƙ...
Tàshìn Bòm Ya Raunata Yara Sama da 5 a Garin Mafa Dake Jihar Borno, daya hannunsa ya cire

Tàshìn Bòm Ya Raunata Yara Sama da 5 a Garin Mafa Dake Jihar Borno, daya hannunsa ya cire

Duk Labarai
Yara 5 ne suka jikkata bayan tashin wani bam a karamar hukumar Mafa dake jihar Borno inda hannun daya daga cikin yaran ya tsinke. Lamarin ya farune ranar alhamis da misalin karfe 2:25 na rana inda yaran suka je suna wasa da Bam din ba tare da sun sani ba. Bam din dai an boyeshi ne a cikin bulo a kusa da inda ake gina Masallacin Juma'a na Mafa. Yaran su 4 ne sai yarinya 1 Abdullahi Umar, Musa Mele, Fatima Abatcha, Abba Kawu Muhammed, da Khalid Alhaji Bukar. Daya daga cikin yaran ya rasa hannun shi inda kuma aka garzsya da guda 4 zuwa Asibitin Maiduguri amma guda daya da hai ji ciwo sosai ba an kaishi Asibitin Mafa inda aka bashi magani aka sallameshi. Tuni 'yansanda da suka kware wajan kwance Bam suna kai dauki wajan.
Kalli Bidiyon yanda Wani Balarabe ya fasa Talabijin dinsa saboda hin Haushin An ci Barcelona

Kalli Bidiyon yanda Wani Balarabe ya fasa Talabijin dinsa saboda hin Haushin An ci Barcelona

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wannan Wani balarabene ya fasa Talabijin dinsa saboda jin Haushin Inter Milan ta fitar da Barcelona a gasar Champions League da aka buga a wannan satin. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1920765965102456856?t=uBQNmtMXseVsDa13mhXKYw&s=19 Wasan dai yayi zafi sosai amma Barca bata yi Nasara ba.
Kalli Bidiyon yanda wata Budurwa ta yi bàtsà a shirin Brekete Family yayin da aka kira ta a waya, sai da kowa ya rike baki saboda abin da ta fada yayi muni

Kalli Bidiyon yanda wata Budurwa ta yi bàtsà a shirin Brekete Family yayin da aka kira ta a waya, sai da kowa ya rike baki saboda abin da ta fada yayi muni

Duk Labarai
Husaini Abdulkadir dan Hajiya wanda shine ke gabatar da shirin Brekete Family ya kira wata matashiya a waya kai tsaye yayin da yake gabatar da shirin. Saidai tana daukar wayar ta fara da maganar Batsa: Kalli Bidiyon: https://twitter.com/Sarki_sultan/status/1920835106450579898?t=EfU5PB3MIZjoICaBr8ss6A&s=19 Da yawa dai sun mata Allah wadai
Sanatocin jihar Kebbi uku sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC

Sanatocin jihar Kebbi uku sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC

Duk Labarai
Sanatocin jihar Kebbi uku sun fice daga jam'iyyar PDP zuwa APC. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sanata Adamu Aliero mai wakiltar Kebbi ta tsakiya da Yahaya Abdullahi mai wakiltar Kebbi ta Arewaa, da kuma Garba Maidoki mai wakiltar Kebbi ta Kudu, suna shirin komawa jam’iyyar, a cewar shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje. Wannan ya biyo bayan ganawar da suka yi da shugaban kasa Bola Tinubu a fadar Aso Rock Villa da ke Abuja, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Kalli Bidiyo: Don Allah Rarara Ka Fadawa Tinubu Mawuyacin Halin Da ‘Yañ Nijeriya Ke Ciki Tunda Yanzu Kai Kadai Yake Jin Maganarsa A Arewa, Inji Sheik Salihu Zaria

Kalli Bidiyo: Don Allah Rarara Ka Fadawa Tinubu Mawuyacin Halin Da ‘Yañ Nijeriya Ke Ciki Tunda Yanzu Kai Kadai Yake Jin Maganarsa A Arewa, Inji Sheik Salihu Zaria

Duk Labarai
Don Allah Rarara Ka Fadawa Tinubu Mawuyacin Halin Da 'Yañ Nijeriya Ke Ciki Tunda Yanzu Kai Kadai Yake Jin Maganarsa A Arewa, Inji Sheik Salihu Zaria. https://twitter.com/Amyrahtu/status/1920862400049279188?t=3Zp4REhKPyNFuB8ywdPHgA&s=19 Da yawa na Kallon Rarara na da fada a wajan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu
A Bari Tinubu Ya Kammala Wa’adinsa Na farko Kafin A Yanke Masa Hukunci, Inji Shugaban Kunhiyar Matasan Arewa, Yerima Shettima

A Bari Tinubu Ya Kammala Wa’adinsa Na farko Kafin A Yanke Masa Hukunci, Inji Shugaban Kunhiyar Matasan Arewa, Yerima Shettima

Duk Labarai
Shugaban kungiyar matasa ta AYCF ya jaddada cewa bai dace a riƙa yanke hukunci kan nasarorin Tinubu ba, duba da cewa bai kammala shekara biyu a ofis ba. Ya roƙi masu sukar gwamnatin Tinubu da su bari ya kammala wa’adin farko kafin su yanke mata hukunci. “Tun farko mun san wa’adin Tinubu zai kasance mai wahala. Ya gaji ƙalubale da ba za a iya warware su cikin shekara guda ba. Ka da mu tayar da jijiyoyin wuya kawai saboda wasu mutane ba su samu muƙaman da suke so ba."
Maganar Gaskiya itace ana Lùwàdì da mutane a Gidan Gyara hali na Goron Dutse saboda ni an tsare ni a gidan kuma na gani>>Inji Wannan matashin

Maganar Gaskiya itace ana Lùwàdì da mutane a Gidan Gyara hali na Goron Dutse saboda ni an tsare ni a gidan kuma na gani>>Inji Wannan matashin

Duk Labarai
A karo na biyu an sake samun wani ya fito ya bayyana cewa, Tabbas ana Luwadi da mutane a gidan yari na Goron Dutse, yace duk wanda yace ba'a yi ba gaskiya ya fada ba. A baya dai an samu wani da ya fito ya fada wanda har aka aika hukumar Hisbah ta yi bincike inda tace ba gaskiya bane. Saidai Shi wannan matashi da ya fito yanzu yace shi an taba tsareshi a gidan Gyara Halin kuma ko da kaishi aka yi, zai nuna masu yi. Saurari Hirarsa: https://twitter.com/northern_blog/status/1920877254915059797?t=DDD-TUKKL7f0DcK_br1_Sg&s=19 Ko da Hisbah suka ce ba gaskiya bane maganar Luwadi da Mutane a Gidan Gyara Hali na Goron Dutse, Mutane da yawa basu yadda dasu ba.
Kalli Bidiyo: Ni Ba Barawo bane shiyasa bana taba kayan Mutane, Kayan Gwamnati kadai nake dauka shima dan nasan ina da hakki a ciki>>Inji Wani Barawo da ‘yansanda suka kama

Kalli Bidiyo: Ni Ba Barawo bane shiyasa bana taba kayan Mutane, Kayan Gwamnati kadai nake dauka shima dan nasan ina da hakki a ciki>>Inji Wani Barawo da ‘yansanda suka kama

Duk Labarai
Wani da ake zarginsu da sata da lalata kayan Gwannati da aka kama ya bayyana cewa shi ba barawo bane. Ya bayyana hakane a yayin da 'yansanda suka yi holinsa yake amsa tambayoyi kan zargin da ake masa. Yace baya son a ce masa Barawo shiyasa baya daukar kayan mutane, yace kayan Gwamnati kawai yake dauka suma dan yasan yana da hakki a ciki. https://twitter.com/northern_blog/status/1920876294683685246?t=NafyQRORCRgORlLUCcNIhQ&s=19 Lamarin dai ya baiwa Mutane Mamaki.