Monday, February 23
Shadow

Duk Labarai

Baka da Tarbiyya>>El-Rufai ya mayarwa da Reno Omokri martani bayan da ya zargeshi da zagin Annabi Isa(AS)

Baka da Tarbiyya>>El-Rufai ya mayarwa da Reno Omokri martani bayan da ya zargeshi da zagin Annabi Isa(AS)

Duk Labarai
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya mayarwa da tsohon Hadimin shugaban kasa, Reno Omokri martani kan sukar da ya masa. Omokri bayan da El-Rufai yace Shugaba Tinubu ne yaki bashi mukamin minista ba majalisa ce taki tantanceshi ba, ya cewa El-Rufai yan da hannu a kisan Kiristoci a kudancin kaduna, da kisan 'yan Shi'a a Zaria, sannan ya zargi El-Rufai da yin barazanar kashe Turawa a kuma zagin Annabi Isa(AS). Saidai a martanin El-Rufai ga Reno Omokri ta shafin X, yace Reno bashi da kunya. Sannan yace Gwamnatin Tinubu ce ta daukeshi aikin kareta wanda abinda ake bukata wajan yin wannan aiki sun hada da rashin da'a, da rashin Tarbiyya da son yin kudi dare daya.
Yakin Basasa da akayi laifin Tsohon Shugaba Yakubu Gowon ne, saboda ya kasa hana kìsàn da akewa Inyamurai a Arewa>>Inji Tsohon shugaban kasa, IBB

Yakin Basasa da akayi laifin Tsohon Shugaba Yakubu Gowon ne, saboda ya kasa hana kìsàn da akewa Inyamurai a Arewa>>Inji Tsohon shugaban kasa, IBB

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, IBB ya bayyana cewa rashin cika alkawari da tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon yayi na kare rayuwar Inyamurai yasa aka fada yakin basasa. Ya bayyana hakanne a cikin littafinsa daya rubuta me suna  ‘Journey in Service’ inda ya kara da cewa, an rika yiwa Inyamurai kisan kiyashi a Arewa duk da alkawarin da Yakubu Gowon yayi na kare rayuwarsu. Yace wannan ne yasa Ojukwu a wancan lokacin yace yace bai yadda ba ana cutar jama'arsa. Yace Tun farko dai Da aka yi juyin mulki Yakubu Gowon ya zama shugaban kasa, Ojukwu yace bai yadda da Yakubu Gowon ya zama shugaban kasa ba saidai Brig Babafemi Ogundipe wanda a wancan lokacin shine soja mafi girman mukami. Saidai Yakubu Gowon yayi ta kokarin ganin ya hada kan sa inda ya k...
Kotu ta daure matashi da ya saci Kaza

Kotu ta daure matashi da ya saci Kaza

Duk Labarai
Kotun Magistrate dake Ago Iwoye, a jihar Ogun ta daure wani matashi me suna Adebanjo Segun dan kimanin shekaru 21 saboda satar kaza. Kakakin Hukumar NSCDC na jihar, Dyke Ogbonnaya ne ya sanar da hakan a wata sanarwa daya fitar ranar Laraba. Lamarin ya farune ranar Laraba, February 19, 2025 inda aka kama matashi Adebanjo. Ogbonnaya ya bayyana cewa, Matashin ya taba aikata hakan a watan Disamba na shekarar 2024 amma aka yafe masa da tunanin cewa shine na farko da ya taba aikatawa. Yace amma a wannan karin an gurfanar dashi a kotu inda kotun ta yanke masa hukuncin daurin watanni 6.
El-Rufai na son kawo rudani a kasarnan>>Inji Wata Kungiyar Arewa

El-Rufai na son kawo rudani a kasarnan>>Inji Wata Kungiyar Arewa

Duk Labarai
Wata Kungiyar Arewa ta bayyana cewa, Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na son kawo rudani a kasarnan. Kungiyar me sunan Arewa Think Tank (ATT) ta bayyana cewa Ba gaskiya bane da El-Rufai ke cewa mutanen Arewa na cike da fushi kan mulkin Tinubu, ta kara da cewa, El-Rufai din ne dai ke son kawo rudani kawai. Kungiyar ta bayyana hakane ta bakin shugabanta, Muhammad Yakubu da aka yi hira dashi a gidan Talana AIT. Ya bayyana cewa, lamarin zaben 2027 da El-Rufai ke magana akai yana son shiga hurumin Allah ne inda yace Allah ne kadai yasan waye zai kai shekarar 2027 din. Ya kuma musanta zargin da El-Rufai yayi na cewa, Nuhu Ribadu na son zama shugaban kasa a shekarar 2031.
Shugaba Buhari ya fadi dalilin da yasa bai halarci babban taron APC ba

Shugaba Buhari ya fadi dalilin da yasa bai halarci babban taron APC ba

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana dalili da yasa bai samu halattar taron masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar APC ba. Da yake magana ta bakin kakakinsa, Malam Garba Shehu, Tsohon shugaban yace takardar gayyatar da aka aika masa an aikata ne a makare shiyasa bai samu zuwa ba. Yace an aikawa Buhari da takardar ranar Litinin amma bata sameshi ba sai ranar Talata, Garba yace ko da jirgin Jet Buhari gareshi ba zai iya halartar taron ba. Saidai yace duk da rashin halartar taron, Shugaba na baiwa Gwamnatinsa goyon bayan da ya kamata.
Matatar Ɗangote ta sake rage farashin man fetur

Matatar Ɗangote ta sake rage farashin man fetur

Duk Labarai
Matatar Man Ɗangote ta sake rage farashin man fetur daga naira 890 a kan lita zuwa naira 825 - wato ragin naira 65 kenan a kan kowace lita ga 'yan kasuwa. A wata sanarwa da ta kamfanin ya fitar a yau Laraba, ya ce ragin zai fara aiki ne daga gobe Alhamis, 27 ga watan nan na Fabarairun 2025. kamfanin ya ce ya yi haka ne domin sauƙaƙa wa al'umma Najeriya, yayin da suke shirin fara azumin watan Ramadana, tare kuma da tallafa wa shirin Shugaba Tinubu na neman farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar ta hanyar rage wa al'ummar ƙasar nauyin kuɗaɗe da ke kansu. Wannan shi ne karo na biyu da matatar take rage farashin man fetur a watan na Fabarairun 2025, inda da farko ta yi ragin naira 60. Haka kuma a watan Disamba na 2024 lokacin bikin Kirsimeti da sabuwar shekara, matatar ta rage farashin ...
Cigaban da Obasanjo, da ‘Yar’adua da Jonathan suka yi bai kai wanda Buhari ya kawo a shekaru 8 ba>>Inji Tsohon Hadimin Buhari, Bashir Ahmad

Cigaban da Obasanjo, da ‘Yar’adua da Jonathan suka yi bai kai wanda Buhari ya kawo a shekaru 8 ba>>Inji Tsohon Hadimin Buhari, Bashir Ahmad

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon hadimin shugaban kasa, Muhammadu Buhari watau Bashir Ahmed ya bayyana cewa ci gaban da jimullar tsaffin Shuwagabannin kasa, Olusegun Obasanjo da Marigayi, Umar Musa 'Yar'adua da Goodluck Jonathan suka kawo bai kai wanda Buhari ya kawo ba a shekaru 8 da yayi yana mulki. Bashir ya bayyana hakane a kafarsa ta Twitter inda yake mayar da martani akan maganar da wani shafin PDP yayi na cewa lokacin karshe da Najeriya ke da dadi inda shafin ya wallafa hotunan tsaffin shuwagab...
Da Duminsa: Zanga-zanga ta barke a Kano

Da Duminsa: Zanga-zanga ta barke a Kano

Duk Labarai
Rundunar 'yansandan Najeriya a jihar Kano ta ce ta kama mutum 17 kan zarginsu da aikata daba da kuma shirya zanga-zanga. Wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce bayanan sirri da ta tattara ne suka ba ta nasarar kama mutanen, amma ba ta bayyana dalilin shirya zanga-zangar ba. Sai dai bayanan da BBC ta tattara sun nuna cewa wasu matasa sun taru a kusa da gidan sarki na Nassarawa, wanda Sarkin Kano na 15 Aminu Ado ke ciki, kafin 'yansanda su tsarwatsa su da safiyar yau Laraba. "Bayan samun bayanan sirri game da shirin zanga-zangar tayar da fitina da wasu ke yi, 'yansanda tare da haɗin gwiwar sauran jami'an tsaro sun fita wasu muhimman wurare a ƙwaryar birnin Kano domin daƙile zanga-zangar," a cewar sanarwar. Har yanzu batun masarautar Kano na ci gaba da jan hankalin mazauna jihar,...
El-Rufai, Amaechi,Buhari, da Osinbajo basu je taron masu ruwa da tsaki na APC ba

El-Rufai, Amaechi,Buhari, da Osinbajo basu je taron masu ruwa da tsaki na APC ba

Duk Labarai
An yi babban taron masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar APC a babban birnin tarayya, Abuja ranar Laraba. An yi taronne a hedikwatar Jam'iyyar dake Abuja wanda shine irinsa na farko tun bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad ya hau mulki. An saka jami'an tsaro sosai a wajan taron kuma masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar da yawa sun halarci taron. Manyan Mutanen da suka halarci wajan taron sun hada da Abdulaziz Yari, Atiku Bagudu, Benjamin Kalu.  Hakanan Gwamnonin jihohin Edo, Benue, Ondo, Ekiti, Kaduna, Jigawa, Nasarawa, Yobe, Niger, Lagos, Kogi, Ogun, da Imo da kuma mataimakin gwamnan jihar Ebonyi duk sun halarci taron. Hakanan tsaffin Gwamnonin jihohin Kogi, Kebbi, Niger, Zamfara, da Plateau duk sun halarci wajan taron. Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, da Mataimakinsa Kashim Shattim...
Da Duminsa: ‘Yan Bìndìgà sun tare ‘yansandan Najeriya sun kashe 2 daga ciki

Da Duminsa: ‘Yan Bìndìgà sun tare ‘yansandan Najeriya sun kashe 2 daga ciki

Duk Labarai
Tawagar 'yansandan Najeriya da suka fita aiki a karamar hukumar Jos dake jihar Filato sun gamu da kwantan baunar 'yan Bindiga inda suka afka musu suka kashe 'yansanda 2. Lamarin ya farune akan titin Little Rayfield Road da misalin karfe 7:30 pm. Ana zargin dai ko 'yan Fashi ko masu garkuwa da mutanene suka afkawa 'yansandan. 'yansandan da aka kashe sune Inspector Fatoye Femi da Inspector Dafur Dashit. An kama daya daga cikin maharan me suna Auwal Ali.