Friday, December 5
Shadow

Duk Labarai

Babbar Sallah: ‘Yan Najeriya na kokawa kan tsadar dabbobi

Babbar Sallah: ‘Yan Najeriya na kokawa kan tsadar dabbobi

Duk Labarai
Babbar Sallah: 'Yan Najeriya na kokawa kan tsadar dabbobi. Yayin da babbar sallah ke ƙara ƙaratowa 'yan Najeriya na kokawa dangane da tsadar dabbobi musamman raguna waɗanda su ne aka fi amfani da su a lokacin layya. Wasu masu sayar da raguna da wakilin BBC a Legas ya tattauna da su sun ce farashin raguna ya ninka sau uku daga yadda aka sani a bara. "Ragon da aka saya a bara naira dubu 100 yanzu ya zama naira dubu 300. Haka shi ma na naira dubu ɗari biyu yanzu ya zama naira ɗari biyar". In ji wani mai sayarwa. Su ma masu sayen dabbobin da dama da aka tattauna da su sun ce bai zama lallai su yi layyar ba duk da dai wasu sun ce "amfani kuɗi shi ne a kashe su ta hanyar da ta dace."
Amurka ta fara janye sojojinta daga jamhuriyar Nijar

Amurka ta fara janye sojojinta daga jamhuriyar Nijar

Duk Labarai
Sojojin Amurka sun fara janyewa daga Nijar kamar yadda tashar talabijin ta ƙasar, Tele Sahel ta rawaito. A wani biki da aka yi a Air Base 101 da ke birnin Yamai, babban hafsan sojojin Nijar, Kanal Maj Mamane Kiaou, ya sanar da cewa, sojojin Amurka 260 daga cikin kiyasin 1,100 da aka kiyasta sun janye daga ƙasar tare da tankunan kayan aiki da dama. Maj Kiaou ya bayar da tabbacin cewa Nijar za ta tabbatar da tsaron jami'an Amurka a lokacin janyewar da ake sa ran kammalawa a tsakiyar watan Satumba. Duk da janyewar, ƙasashen biyu sun fitar da sanarwar hadin gwiwa a ranar 8 ga watan Yuni, inda suka tabbatar da cewa dangantakarsu ba za ta ɓaci ba. Janyewar sojojin ta biyo bayan sanarwar da gwamnatin mulkin sojan Nijar ta bayar a ranar 16 ga watan Maris, inda ta soke yarjejeniyar da t...
Gwamnatin jihar Plateau ta ɗage dokar hana yawo a Mangu

Gwamnatin jihar Plateau ta ɗage dokar hana yawo a Mangu

Tsaro
Gwamnatin jihar Filtao ta bayar da sanarwar dage dokar hana yawo da ta saka tun a watan Janairun wannan shekara a karamar hukumar mulki ta Mangu da kewaye. Gwamnan jihar Caleb Mutfwang ne ya saka dokar hana fitan har na tsawon awa ashirin da hudu a kowace rana, bayan wani hari da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a kauyukan Punshit da Sabon-Gari inda suka kashe akalla mutum sha uku tare da jikkata karin wasu baya ga kona gidajen jama’a da dama. Gwamnatin Filaton ta bayyana cewa an saka dokar ne domin a samar da cikakken tsaro da zaman lafiya tsakanin kabilu daban-daban da ke fadin jihar.
Blinken a Masar don inganta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Blinken a Masar don inganta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Duk Labarai
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya isa Masar domin samun goyon bayan yankin ga yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da shugaba Joe Biden ya gabatar kwanan nan. Wannan ziyarar dai ita ce ziyara ta takwas da Blinken ya kai yankin Gabas ta Tsakiya tun bayan ɓarkewar rikicin Gaza. Blinken zai gana da shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi kafin ya tattauna da firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a yau Litinin. Masu shiga tsakani a yankin ciki har da Qatar, sun shafe watanni da dama suna ƙoƙarin sasantawa tsakanin Isra'ila da Hamas. Netanyahu ya ci gaba da jajircewa wajen ƙin amincewa da duk wani tsagaita bude wuta har sai an wargaza sojojin Hamas da kuma sako duk waɗanda aka yi garkuwa da su. A karshen makon da ya gabata, sojojin Isra'ila sun kuɓutar da wasu mutane hu...
Ji yanda sojan Najeriya da aka yi gar-ku-wa dashi ya kwace Bin-di-gar maharan ya kubutar da kanshi da sauran mutane

Ji yanda sojan Najeriya da aka yi gar-ku-wa dashi ya kwace Bin-di-gar maharan ya kubutar da kanshi da sauran mutane

Tsaro
Wani sojan Najeriya me mukamin Kyaftin yayi abin yabo inda ya kubutar da kansa da wansu sauran mutane da aka yi garkuwa dasu tare. Sojan me suna Captain J.O. Abalaka Ya kubutar da kansa ne a jihar Kogi bayan da aka yi garkuwa dashi. Lamarin ya farune makon da ya gabata a yayin da sojan ke kan hanyar zuwa Borno inda aka mayar dashi daga Jihar Rivers inda yake aiki. Sojan na cikin motarsa me kirar Toyota Corolla tare da karensa yayin da lamarin ya faru, saidai ya yi nasarar kwace bindigar AK47 daga hannun daya daga cikin 'yan Bindigar inda ya kori sauran. Sojan ya kuka kwace bindiga kirar hannu da sauran wasu abubuwa.

Sau nawa ake jima’i: Sau nawa ya kamata ayi jima’i

Duk Labarai, Jima'i, Kiwon Lafiya
Wani bincike ya nuna cewa yin jima'i sau daya a sati yana baiwa ma'aurata natsuwa. Hakanan kuma wasu masana halittar dan adam sun bayyana cewa, yin jima'i kasa da sau 10 a shekara na nufin cewa ma'aurata na cikin auren da babu jima'i, watau hakan yayi kadan matuka. Saidai kuma wani bincike ya nuna cewa, idan aka yi sabon aure, yayin da suke amarya da ango, ma'aurata kan yi jima'i kusan har sau 3 ko 4 a rana. Hakanan, idan ma'aurata na son samun haihuwa, shima sukan yi jima'i da yawa da tunanin ko ciki zai shiga. Magana mafi inganci itace, babu wata matsala idan mutum na yin jima'i a kullun. Masana sunce, Jima'i na saka mutum farin ciki nan take kuma yana yayewa mutum damuwa. Jima'i yakan iya zama yana da illa ne kawai idan: Ya zamana ya hana ka yin ayyukan ci gaban ra...
Da Duminsa: Majalisar Tarayyar Najeriya ta nemi a canja tsarin mulki da zai baiwa shugaban kasa damar yin zango daya na shekaru 6

Da Duminsa: Majalisar Tarayyar Najeriya ta nemi a canja tsarin mulki da zai baiwa shugaban kasa damar yin zango daya na shekaru 6

Siyasa
Wasu 'yan majalisar wakilai sun nemi cewa, a canja tsarin mulkin Najeriya da zai baiwa shugaban kasa damar yin mulki na shekaru 6 wa'di daya. Sannan sun nemi a rika yin karba-karbar mulki tsakanin yankuna 6 da ake dasu a kasarnan. Dan majalisar daga jihar Imo, Ikenga Ugochinyere ne ya bayyana hakan inda yace idan shugaban kasa, Gwamnoni suka rika yin wa'adi daya na shekaru 6 kawao, za'a samu saukin kashe kudi da kuma yin aiki me kyau.
PDP Ta Sanya Ranar Da Za ta Yi Taron NEC Karo Na Biyu

PDP Ta Sanya Ranar Da Za ta Yi Taron NEC Karo Na Biyu

Siyasa
PDP Ta Sanya Ranar Da Za ta Yi Taron NEC Karo Na Biyu Jam’iyyar PDP ta bayyana ranar Alhamis 26 ga watan Satumba a matsayin ranar da za ta gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa karo na biyu a shekarar 2024. Idan za a iya tunawa, a taron farko da hukumar NEC ta gudanar a ranar 18 ga watan Afrilu,an tattauna batutuwan da suka hada da makomar mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Illiya Damagum, an daga shi zuwa taron NEC na gaba wanda aka shirya tun watan Agusta. Kungiyar ‘yan jam’iyyar ta Arewa ta tsakiya ta ce za a zabi dan takara daga shiyyar don kammala wa’adin tsohon shugaban Jam'iyyar na kasa, Dr. Iyiorchia Ayu, wanda ya yi murabus kusan shekaru biyu cikin wa'adinsa na shekaru hudu. Gabanin taron NEC na watan Satumba, jam’iyyar ta tsayar da ranar 27 ga wata...
ƳANZU-YANZU: Za a fassara huɗubar Arfa da Hausa, Cewar Sheikh Sudais

ƳANZU-YANZU: Za a fassara huɗubar Arfa da Hausa, Cewar Sheikh Sudais

Siyasa
Babban Limamin Masallatan Harami Sheikh Abdurrahman Sudais ya sanar cewa za a fassara hudubar Ranar Arafa kai-tsaye a cikin harshen Hausa da wasu harsuna 19 domin karuwar alhazai da sauran al'ummar Musulmi a fadin duniya. Sheikh Sudais ya ce ana sa ran sama mutum miliyan 100 za su saurari hudubar wadda Sheikh Maher Al Mu'ayqaly zai gabatar a Masallacin Namirah ta kafofin watsa labarai daban-daban.