Friday, December 5
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki

Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki

Siyasa
Kungiyar Kwadago, NLC ta bayyana cewa bata akince da tayin Naira dubu 62 a matsayin mafi karancin Albashi ba. Tace kai ko dubu 100 ba zata amince dashi a matsayin mafi karancin Albashin ba, Kungiyar tace wannan kudi sun yi kadan wa ma'aikata su rayu ciki rufin asiri. Mataimakin babban sakataren kungiyar, Chris Onyeka ne ya bayyana haka a Channels TV yayin ganawa dashi ranar Litinin. Ya kuma ce kwaki 7 ko sati daya da suka baiwa gwamnati kan ta bayyana matsayinta ya kare ranar Talata, kuma idan gwamnatin ta dage akan hakan, zasu sake zama ranar talatar dan tsayar da matsaya kan ci gaba da yajin aikin. “Our position is very clear. We have never considered accepting N62,000 or any other wage that we know is below what we know is able to take Nigerian workers home. We will not nego...
An sace dalibai da wasu 25 a hanyar zuwa Nasarawa

An sace dalibai da wasu 25 a hanyar zuwa Nasarawa

Tsaro
Rahotanni sun bayyana cewa, an yi garkuwa da mutane 25 da kuma wasu dalibai akan hanyar Abuja zuwa Nasarawa. Lamarin ya farune ranar Juma'a kamar yanda jaridar Punch ta ruwaito kuma yawan wadanda aka yi garkuwa dasu sun kai 30. Direban motar dai ya kubuta inda ya kaiwa 'yansanda rahoton faruwar lamarin. Hukumar 'yansanda ta jihar Nasarawa ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakinta,Rahman Nansel inda tace an kubutar da mutane 3 daga cikin wadanda aka yi garkuwa dasu kuma ana kan kokarin kubutar da sauran.
Kasar Rasha na takurawa ‘yan Afrika dake kasarta, ko dai su shiga aikin soja, su je yaki da Ukraine ko kuma ta dawo dasu gida

Kasar Rasha na takurawa ‘yan Afrika dake kasarta, ko dai su shiga aikin soja, su je yaki da Ukraine ko kuma ta dawo dasu gida

Siyasa
Rahotanni daga kasar Rasha na cewa, kasar na takurawa 'yan Afrika dake kasar shiga aikin soji dan yin yaki da kasar Ukraine. Rahoton jaridar Bloomberg ya bayyana cewa, kasar ta Rasha tana kuma takurawa hadda dalibai dake karatu a kasar. Saidai duk da haka wasu na baiwa jami'an tsaro cin hanci dan su kyalesu su zauna a kasar ba tare da su shiga aikin sojan ba ko kuma an dawo dasu gida ba. Yakin Rasha da Ukraine dai kullun sai kara kazancewa yake inda Ukraine din ke ci gaba da samun goyon bayan kasashen Yamma da Amurka.
Bai kamata Tinubu ya soki Gwamnatin Buhari ba saboda cewa yayi zai dora daga inda Buhari ya tsaya>>Buba Galadima

Bai kamata Tinubu ya soki Gwamnatin Buhari ba saboda cewa yayi zai dora daga inda Buhari ya tsaya>>Buba Galadima

Siyasa
Jigo a jam'iyyar NNPP, Injiniya Buba Galadima ya bayyana cewa, bai kamata shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dorawa Buhari ko wane irin laifi ba. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a jaridar Sunnewsonline. Yace dalilin da yasa yace haka shine Tinubu yayi Alkawrin dorawa akan inda shugaba Buhari ya gama mulkinsa. Da aka tambayeshi ko me zai ce kan matsin rayuwar da ake ciki, Buba Galadima ya kada baki yace ai 'yan Najeriya ne suka siyowa kansu da kudinsu. Yace sai da ya gargadi mutane amma suka kiya.
Kalli Hotunan wata maboyar ‘yan Bin-di-ga da ‘yansanda suka gano

Kalli Hotunan wata maboyar ‘yan Bin-di-ga da ‘yansanda suka gano

Abuja, Tsaro
'Yansanda a Abuja sun bankado wata maboyar 'yan Bindiga dake gidan Dogo a cikin daji Kweti dake kusa da babban birnin tarayya, Abuja. Kakakin 'yansandan Abuja, SP Josephine Adeh ta bayyana hakan ga manema labarai inda tace an bankado maboyar ne bayan samun bayanan sirri. An kama mutane 4 da ake zargi bayan da aka yi musayar wuta tsakaninsu da jami'an tsaron. Dukansu sun amsa cewa su masu garkuwa da mutanene. An kubutar da wasu da suka yi garkuwa dasu inda aka mika su hannun 'yan uwansu.
Ji yanda ake ciki kan maganar mafi karancin Albashi tsakanin Gwamnati da NLC, inda ake tunanin za’a sake komawa yajin aiki

Ji yanda ake ciki kan maganar mafi karancin Albashi tsakanin Gwamnati da NLC, inda ake tunanin za’a sake komawa yajin aiki

Siyasa
Tattaunawa na ci gaba da gudana tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar kwadago ta NLC da TUC inda ake tsammanin za'a karkare a yau. Kungiyar tace ta gabatarwa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da bukatarta ta a biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin albashi kuma tana jiran ta ji amsa daga gareshi. Saidai matsayar gwamnati shine biyan Naira 62,000 a matsayin mafi karancin Albashin. Shuwagabanni kwadagon sun je Geneva, Kasar Switzerland inda suke halartar taro kan kungiyoyin kwadago na Duniya. Kuma ana tsammanin bayan aun kammala taron, zasu dawo a samu matsaya kan mafi karancin Albashin.
Kalli yanda ‘yan Najeriya suka koma amfani da Cucumber/Gurji wajan yin miya maimakon Tumar saboda tsadar Tumatir din

Kalli yanda ‘yan Najeriya suka koma amfani da Cucumber/Gurji wajan yin miya maimakon Tumar saboda tsadar Tumatir din

Duk Labarai
'Yan Najeriya da yawa sun koma amfani da Gurji, ko kuma Cucumber maimakon Tumatur wajan yin miya. Tumatur dai yayi tsadar da ba'a yi tsammani ba inda ya gagari talaka. An ga yanda aka rika yin miya da Gurji maimakon Tumaturin. https://twitter.com/chude__/status/1799835716891127967?t=oFUgU136aLx5ZXXbp4rUzw&s=19 Me zaku ce?
Suma Sanatoci Mafi karancin Albashi ya kamata a biyasu>>Inji Father Mbaka

Suma Sanatoci Mafi karancin Albashi ya kamata a biyasu>>Inji Father Mbaka

Siyasa
Babban malamin Kirista, Father Ejike Mbaka ya bayyana cewa, kamata yayi suma 'yan majalisar tarayya a rika biyansu mafi karancin Albashi. Ya bayyana cewa ma'aikata dakw ainahin wahala wajan aiki amma sune ake biya kudade 'yan kadan inda yace sam hakan bai dace ba. Yace a mayar da mafi karancin Albashin a rika biyan kowa dashi har 'yan majalisar kada a mayar da wasu bayi. Yace saboda menene za'a rika biyan 'yan majalisar Alawus wanda ya wuce ka'ida?
Mu fa har yanzu muna nan kan matsayin mu sai Gwamnati ta biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin Albashi>>NLC

Mu fa har yanzu muna nan kan matsayin mu sai Gwamnati ta biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin Albashi>>NLC

Siyasa
Kungiyar kwadago ta NLC ta jaddada matsayinta na cewa sai Gwamnatin tarayya ta biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin Albashi. Shugaban NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana haka a inda yace suna jiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauki mataki kan lamarin. Gwamnatin tarayya dai tace Naira 62,000 ne zata iya biya a matsayin mafi karancin Albashin. Saidai Gwamnoni sunce au bazama su iya biyan hakan ba idan dai ba duka kudaden da suke samu bane zasu rika biyan Albashi dashi ba. Yanzu dai abin jira a gani shine yanda zata kaya.