Ka dakatar da shirin shigo da kayan abinci daga kasar waje, saboda tabbas farashin kayan abinci zai yi sauki amma mu kuma kasuwancin mu zai lalace>>’Yan kasuwar Najeriya suka roki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shan matsin lamba akan lallai sai ya dakatar da cire harajin da yace zai yi akan kayan abinci da na magani da sauransu da ake shigowa dasu daga kasashen waje saboda kayan su yi sauki, 'yan Najeriya su siya da Arha.
Majiyoyi da yawa daga fadar shugaban kasar sun tabbatar da wannan batu inda suka ce 'yan kasuwa da kamfanoni masu zaman kansu ne suke matsawa shugaban kasar akan lallai ya janye wannan abu da yake son gudanarwa.
Suna bada dalilin cewa idan shugaban yace sai yayi hakan, to lalai zai dakushe zuba jari a Najeriya kuma za'a rasa ayyukan yi.
Hakanan wasu daga cikin kamfanonin da 'yan kasuwar sun tabbatar da wannan batu inda suka ce idan shugaban kasar ya cire harajin aka fara shigo da kayan daga kasashen waje suka yi sauki a Najeriya, to s...








