Wednesday, February 18
Shadow

Duk Labarai

Wata Sabuwa: Iyalan marigayi Shugaban sojojin, Lagbaja sun yi zargin cewa kasheshi aka yi

Wata Sabuwa: Iyalan marigayi Shugaban sojojin, Lagbaja sun yi zargin cewa kasheshi aka yi

Duk Labarai
Kanin Mahaifin marigayi shugaban sojojin kasa na Najeriya, Lt. General Taoreed Lagbaja me suna Pa Tajudeen Lagbaja ya bayyana cewa, yana dana sanin sayarwa shugaban sojojin fom din shiga soja da yasan hakan zai yi sanadiyyar mutuwarsa. Wasu Dangin shugaban sojojin sun yi zargin cewa an kashe shi ne ta hanyar tsubbu wanda ya samo Asali daga wani rikicin Fili a mahaifarsa. Kanin mahaifin nasa yace mutuwar data dauki shugaban sojojin, shi ya kamata ace ta dauka. Ya yabeshi a matsayin wanda ya rika tallafawa mutane kowa da kowa.
Wata Sabuwa Bidiyo ya bayyana, Ashe matar mutuminnan dan kasar Equatorial Guinea da yayi lalata da mata 400 shima gana cin Amanarsa

Wata Sabuwa Bidiyo ya bayyana, Ashe matar mutuminnan dan kasar Equatorial Guinea da yayi lalata da mata 400 shima gana cin Amanarsa

Duk Labarai
Lamari dai ya kara rinchabewa Baltasar Engonga shugaban hukumar yaki da rashawa ta kasar Equatorial Guinea wanda Bidiyon sa guda 400 suka bayyana yana lalata da matan aure. To ashe dai shima matarsa tana cin amanarsa. Bidiyo ya bayyana a shafukan sada zumunta inda aka ga matar itama tana lalata da wani mutum. Lamarin dai ya bayar da mamaki. An dai kori Baltasar daga aiki inda aka kuma kamashi aka gurfanar dashi a kotu. Kasancewar Bidiyon matar shima akwai tsiraici da yawa,Shafin hutudole ba zai iya kawo muku shi a nan ba.
Sabuwar kungiyar dake ikirarin Jìhàdì me suna Làkùràwà ta karbe iko da kananan hukumomi 5 a jihar Sokoto

Sabuwar kungiyar dake ikirarin Jìhàdì me suna Làkùràwà ta karbe iko da kananan hukumomi 5 a jihar Sokoto

Duk Labarai
Sabuwar kungiyar dake ikirarin Jihadi me suna Lakurawa a jihar Sokoto ta karbe iko da wasu bangarori na kananan hukumomi 5 a jihar Sokoto inda take karbar Haraji da Zakka. Kananan hukumomin da Kungiyar ta kama iko da su sun hada da Tangaza, Gada, Illela, Silame, da Binji kamar yanda wata majiya ta bayyanawa jaridar Vanguard. Rahoton yace wannan kungiya ta Lakurawa na magana da yarukan Hausa, Fulani, Tuareg, Kanuri, Tuba, da Turanci. Rahoton yace mutanen na zuwane a babura inda sukan bar wasu su musu gadi sannan su tafi wani garin. Shugaban karamar hukumar Tangaza, Alhaji Isa Salihu Kalenjeni ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace ko da kwanannan sai da suka kwacewa wani dan kasuwa Naira Miliyan 2 sannan suka kwace masa mota sai da ya biya Naira 350,000 sannan suka bar masa i...
Matatar man fetur din Dangote zata fara fitar da man fetur din zuwa kasashen Africa guda 7

Matatar man fetur din Dangote zata fara fitar da man fetur din zuwa kasashen Africa guda 7

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Matatar man fetur ta Dangote zata fara fitar da man fetur din zuwa kasashen Africa 7. A yanzu dai matatar ta shirya tsaf dan fara fitar da man fetur din zuwa kasashen South Africa, Angola, da Namibia. Sannan kuma tana tattaunawa da kasashen Niger Republic, Chad, Burkina Faso da Central Africa Republic dan fara kai musu man fetur din. Hakana wata majiya tace akwai karin kasashe da ake sa ran zasu bayyana son daukar man fetur din na Dangote. Misali kasar Ghana ma an bayyana cewa tana son fara magana da Dangote dan fara sayen man fetur dinsa. Shugaban hukumar kula da man fetur ta kasar Ghana,Mustapha Abdul-Hamid ya bayyana cewa fara siyen man fetur din daga hannun Dangote zai sa su daina sayen man fetur din daga kasashen Turai
Farashin kayan abinci ya tashi a kasuwannin Duniya

Farashin kayan abinci ya tashi a kasuwannin Duniya

Duk Labarai
Farashin kayan abinci sun yi tashin gwauron zabi a kasuwannin Duniya inda suka yi tsadar da ba'a taba ganin irin ta ba a cikin watanni 18. Abinda yafi daukar hankali shine farashin man girki. Farashin man girkin ya karu da kaso 7.3 wanda ba'a taba ganin irin wannan tsada ba a cikin shekaru 2 da suka gabata. shi kuma Sukari ya tashi da kaso 2.6 Sai madara ta tashi da kaso 2.5 Farashin Namane kawai ya bai sauka ba.
Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja

Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja

Duk Labarai
Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja {"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja Wace fata za ku yi mata?