Tuesday, February 17
Shadow

Duk Labarai

Ƴansanda sun gurfanar da masu zanga-zanga kan cin amanar ƙasa a jihar Borno

Ƴansanda sun gurfanar da masu zanga-zanga kan cin amanar ƙasa a jihar Borno

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan Najeriya reshen jihar Borno ta gurfanar da mutum 19 da suka haɗa da wasu ƙananan yara uku a gaban kotu bisa zargin hannunsu a zanga-zangar tsadar rayuwa a watan Agusta. An gurfanar da su ne a gaban Mai Shari’a Aisha Mohammed Ali a babbar kotun jihar da ke birnin Maiduguri a yau Litinin, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. Wannan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da ake matsa wa gwamnatin tarayya lamba kan ta janye tuhumar da ake yi wa ƙananan yara da aka kama saboda gudanar da zanga-zangar. A cewar takardar da aka gabatar a kotun, yaran uku suna tsakanin shekaru 14 zuwa 17. Gwamnatin jihar Borno ta gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume biyu da suka haɗa da cin amanar ƙasa, da kuma amfani da kafafen sada zumunta wajen ɓat...
Da Duminsa: Tinubu ya ba da umarnin sakin yaran da aka gurfanar a kotu kan zanga-zanga

Da Duminsa: Tinubu ya ba da umarnin sakin yaran da aka gurfanar a kotu kan zanga-zanga

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayar da umarnin sakin dukkan ƙananan yaran da aka kama da zargin cin amanar ƙasa sakamakon shiga zanga-zanga kan tsadar rayuwa. Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris ya ce an kuma kafa wani kwamati da zai bincika yadda aka kama su da sauran lamurransu. "Shugaban ƙasa ya ce a sake su kuma a sadar da su ga iyayensu," in ji ministan lokacin da yake magana manema labarai a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja. Bayanan sun fito ne jim kaɗan bayan kammala rantsar da sababbin ministoci bakwai da Shugaba Tinubu ya naɗa a fadarsa a yau Litinin. Kwamatin da zai yi aikin zai kasance ƙarƙshin ma'aikatar agaji da rage talauci, in ji ministan.
Remi Tinubu da Ribadu za su jagoranci yi wa Najeriya addu’a dan ta fita daga matsalar tsananin Rayuwa

Remi Tinubu da Ribadu za su jagoranci yi wa Najeriya addu’a dan ta fita daga matsalar tsananin Rayuwa

Duk Labarai
Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu za su jagoranci addu'a ta musamman domin neman sauƙin matsalolin da Najeriya ke fuskanta. Za a gudanar da addu'ar ne ƙarƙashin jagorancin jagororin addinin Musulunci da Kirista, domin neman taimakon Allah a kan ƙalubalen da suka yi ƙasar dabaibayi. Chief Segun Balogun Afolorunikan, wanda shi ne darakta-janar na shirya addu'ar ta ƙasa ne ya sanar da hakan a Abuja, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito. Ya ce akwai buƙatar kowa ya bayar da nasa gudunmuwar domin magance matsalar da ƙasar ke fuskanta, inda ya nanata cewa haɗin kai na da muhimmanci wajen shawo kan dukkan matsala. "Bayan addu'ar, muna da yaƙinin Allah zai buɗe mana hanyoyin da za mu samu sauƙi," Afolo...
Farashin kayan Abinci zasu tashi a Najeriya saboda babu Network a bankuna

Farashin kayan Abinci zasu tashi a Najeriya saboda babu Network a bankuna

Duk Labarai
Matsalar rashin Network a bankunan Najeriya yasa ake tsammanin samun hauhawar farashin kayan abinci. Manyan jiragen ruwa sun kawo abunci kala-kala daga kasashen waje inda suke gabar tekun Legas suna jira a kammala duk takardunsu na haraji wadanda suka makale a bankuna saboda matsalar rashin Network. Rahoton daga jaridar Naigerian Tribune yace kayan auna kan ruwa inda masu kayan suke jiran takardunsu, inda matsalar take shine duk kwana daya da kayan suka kara sai mai kaya ya sake biyan kudin haya na Kwantena da kayansa suke ciki. Wakilin masu kawo kayan Mr. Frank Ogunojemite ya bayyana cewa, suna bukatar gwamnati ta rika basu wani dauki ko tallafi a irin wannan yanayi saboda ba laifinsu bane. Yace duka kudin hayar da suka biyawa kayan nasu akan wanda zasu sayi kayan zasu fanshe...
Kalli Hotuna da Bidiyo sun bayyana na wannan dan kasuwar yana lalata da matan manyan mutane

Kalli Hotuna da Bidiyo sun bayyana na wannan dan kasuwar yana lalata da matan manyan mutane

Duk Labarai
Wannan mutumin wanda dan kasuwane dan kasar Equatorial Guinea ya shiga idon duniya bayan da bidiyo sama da guda 400 suka bayyana inda suka nunashi yana lalata da mata. Wani abin karin ban mamakin shine cikin matan da yayi lalata dasu hadda matan aure da kuma matan manyan 'yansiyasa na kasar. Rahotanni sun ce cikin matan manyan mutanen da yayi lalata dasu akwai matar ministan shari'a na kasar, da matan sauran ministoci. Akwai kuma matar kaninsa. Da matar kawunsa. Da matar Faston cocin da yake halarta. Da matar uban gidansa. Da matar me tsaron lafiyarsa. Da abokan kanwarsa da dai sauransu. Rahoton yace mutumin baya amfani da kwandam wajan yin lalata da matan. Tuni dai an garzaya dashi kotu inda kotun tace a je a gwadashi ko yana dauke da cutar dake yaduwa ta...
Mu talakawa ne ba za mu iya yin belin yaranmu ba – Iyayen yaran da aka tsare

Mu talakawa ne ba za mu iya yin belin yaranmu ba – Iyayen yaran da aka tsare

Duk Labarai
Iyalan yaran da aka tsare kan zargin yin zanga-zanga a Kano da Kaduna sun koka kan a yi masu adalci. Iyaye da ƴan uwan yaran sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa yaran su basu da hannu kan zargin da ake masu na cin amanar ƙasa, inda suka roƙi hukumomi da su sakar masu ƴaƴansu. Mutanen sun bayyyana cewa su talakawa ne basu da ƙarfin da za su cika dukkan sharuddan beli da kotu ta bayar a Abuja. An kama masu zanga-zangar 76 a lokacin da aka yi zanga-zangar tsadar rayuwa daga ɗaya zuwa 10 ga watan Agusta, inda aka gurfanar da su a gaban babbar kotun Abuja a ranar Juma'a. Al'umma a faɗin Najeriya na ci gaba da bayyana takaicinsu kan bidiyon yaran da aka gurfanar gaban kotu daga wasu jihohin arewacin ƙasar. Yaran waɗanda gwamnati ta zarga da cin amanar ƙasa, sun bayyan...
Tinubu ya rantsar da sababbin ministoci

Tinubu ya rantsar da sababbin ministoci

Duk Labarai
Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya rantsar da sababbin ministocin da ya naɗa a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja. Da yake jawabi jim kaɗan bayan rantsar da su, Tinubu ya ce, "mun fara ƙoƙarin dawo da tattalin arzikinmu cikin hayyacinsa," in ji shi, sannan ya ƙara da cewa, "muna kan tafarki mai kyau domin cika burinmu, ba ma don mu kaɗai ba, har da jin daɗin ƴaƴanmu da jikokinmu." Shugaban ƙasan ya ce duk da ƙalubalen da ake fuskanta, ana ci gaba da aikin inganta tattalin arzikin ƙasar. Sai ya bayyana wa sababbin ministocin cewa an zaɓo su domin su bayar da gudunmuwarsu domin ceto ƙasar. A ranar 23 ga Oktoba ce Tinubu na cire wasu ministoci guda biyar, sannan ya naɗa wasu guda bakwai. A ranar 30 ga Oktoba kuma Majalisar Dattawa ta tantance tare da amincewa da sababbin ministocin wato...
Rikicin Jam’iyyar NNPP: Gwamna Abba Gida-Gida yaki daga waya bayan sa Kwankwaso ya kirashi

Rikicin Jam’iyyar NNPP: Gwamna Abba Gida-Gida yaki daga waya bayan sa Kwankwaso ya kirashi

Duk Labarai
Rikicin cikin gida na jam'iyyar NNPP na kara kazanta bayan sa rahotanni suka bayyana cewa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf yaki daukar wayar Kwankwaso bayan da ya kirashi kuma yaki halartar taron ganawa da Kwankwason. Sarar Abba Tsaya da kafarka wadda ke nufin Abba ya raba gari da Kwankwaso na kara samun yaduwa a siyasar ta Kano. Jam'iyyar ta rabu gida biyu inda wasu ke son a hada kai da APC a matakin tarayya, wasu kuma sun je kotu suna son a basu iko da shugabancin jam'iyyar dan kwace ragamarta daga hannun Kwankwaso. Rahoton jaridar Daily Nigerian ya bayyana wanda ke kokarin ganin sun zuga Abba ya bijirewa Kwankwaso kamar haka: Sakataren Gwamnatin Jihar, Baffa Bichi. Kwamishinan Tafiye-tafiye, Mohammed Diggol. Kwamishinan Ilimi, Umar Doguwa. Sanatan dake wakilta...
A karshe dai da daudu Bobrisky ya samu fita daga Najeriya bayan da aka kamashi

A karshe dai da daudu Bobrisky ya samu fita daga Najeriya bayan da aka kamashi

Duk Labarai
Shahararren dan daudu, Idris Okuneye wanda aka fi sani da Bobrisky ya samu fita daga Najeriya kwanaki kadan bayan da aka kamashi amma aka bayar da belinsa. Ana dai zargin Bobrisky da laifin rashawa da cin hanci ne Bobrisky ya bayyana fitarsa daga Najeriya ne zuwa kasar waje ta hanyar shafinsa na sada zumunta saidai bai fadi kasar da ya tafi ba. Yace Naira Miliyan 30 ya kashe wajan siyan tikitin jirgin First Class. A baya dai an ga yanda aka kama Bobrisky aka fitar dashi daga cikin jirgi da karfin tsiya a yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Birnin Landan na kasar Ingila. Daga baya ta bayyana cewa hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC ce ta kamashi. Daga baya an daukeshi daga Legas zuwa Abuja. Kuma hukumar ta EFCC ta bayyana cewa ta kamashine saboda yaki amsa gayyatar d...
Najeriya ta zo ta 5 a Duniya wajan yawan masu amfani da kafafen sada zumunta

Najeriya ta zo ta 5 a Duniya wajan yawan masu amfani da kafafen sada zumunta

Duk Labarai
Najeriya ta haura zuwa matsayi na 5 a Duniya a cikin kasashen da suka fi amfani da kafafen safa zumunta. Kafafen Cable.co.uk da We Are Social ne suka bayyana hakan a wata sanarwa da suka fitar. A bayanin an ga cewa, 'yan Najeriya na yin akalla awanni 3 da mintuna 23 akan kafafen sada zumunta. Kasar Kenya ce ta zo ta daya sai kasar Kasar Africa ta kudu ke take mata baya inda kasar Brazil ta zo ta uku sai kasar Philippines ta zo ta 4. Ga jadawalin kasashen da suka fi yawan Amfani da kafafen sadarwar zamanin kamar haka: Kenya – 03:43 South Africa – 03:37 Brazil – 03:34 Philippines – 03:33 Nigeria – 03:23 Colombia – 03:22 Chile – 03:11 Indonesia – 03:11 Saudi Arabia – 03:10 Argentina – 03:08 Mexico – 03:04 Malaysia – 02:48 Ghana – 02:43 Egy...