Saturday, January 3
Shadow

Duk Labarai

Kalli Hoto: Tsohuwar ‘yar kwallon Najeriya da Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru Ahmad ya dauki nauyinta zuwa kasar Amurka aka mata aiki ta koma Namiji na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan a mata karin aikin da zata rika haihuwa

Kalli Hoto: Tsohuwar ‘yar kwallon Najeriya da Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru Ahmad ya dauki nauyinta zuwa kasar Amurka aka mata aiki ta koma Namiji na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan a mata karin aikin da zata rika haihuwa

Duk Labarai
Tsohuwar 'yar kwallon Najeriya, Iyabo Abade wadda yanzu Namiji ce da sunan James Johnson na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan ta samu ta rika haihuwa. Iyabo ta bugawa Najeriya was a tsakanin 1997 da 2000. Kuma a shekarar 2004 ne aka canja mata halitta a kasar Amurka ta koma Namiji. Tsohon ministan babban birnin tarayya a wancan lokacin, Malam Nasiru El-Rufai ne ya dauki nauyin aikin da aka mata. Saidai kamin kace wani abu, Ita dai Iyabo an haifeta ne a matsayin mata maza, watau tana da azzakari da farji irin na mata. Dan hakane ta zabi daya ko kuma aka duba wanda yafi karkata aka gano Namiji ne kuma aka mata aiki ta koma cikakken Namiji. Saidai tana bukatar a kara mata aiki dan ta samu ta rika haihuwa.
Akwai yiyuwar a yi fama da wahalar man fetur yayin da kungiyar NUPENG ke shirin bin kungiyar kwadago itama ta yi yajin aiki

Akwai yiyuwar a yi fama da wahalar man fetur yayin da kungiyar NUPENG ke shirin bin kungiyar kwadago itama ta yi yajin aiki

Siyasa
Kungiyar ma'aikatan man fetur ta NUPENG ta umarci membobinta da su shiga yajin aikin sai mama ta gani wanda za'a fara a gobe Litinin. Sakataren Kungiyar, Mr Afolabi Olawale ne ya bayyana haka inda yace kungiyar tasu zata bi umarnin yajin aikin. Kungiyoyin NLC da TUC dai sun bayyana aniyar shiga yajin aiki a gobe litinin wanda sai abinda hali yayi kan neman gwamnati ta kara mafi karancin Albashi. Wannan mataki na NUPENG dai zai iya jefa da yawa daga cikin 'yan Najeriya cikin matsalar wahalar man fetur.

Idan aka biya ma’aikata mafi karancin Albashin da suke nema na Naira N494,000 sauran mutanen Najeriya zasu shiga wahala>>Ministan Yada Labarai

Siyasa
Ministan yada labarai, Mohammed Idris ya bayyana damuwa kan bukatar kungiyar NLC ta a biyasu mafi karancin Albashi na Naira N494,000. Ministan yace idan aka biya wannan mafi karancin Albashin da kungiyar NLC take nema, za'a rika kashe Naira N9.5 trillion wajan biyan Albashi. Ya kara da cewa kuma hakan zai jefa rayuwar sauran 'yan Najeriya miliyan 200 cikin wahala. A zama na karshe dai da aka yi tsakanin kungiyar ta Kwadago da Gwamnati an tsaya ne akan gwamnati zata biya Naira Dubu 60 a matsayin mafi karancin Albashi wanda kungiyar Kwadagon tace bata yadda ba. Hakan yasa kungiyar tace tunda dai ba'a cimma matsaya tsakaninta da gwamnati ba, zata shiga yajin aikin sai mama ta gani daga ranar Litinin dinnan me zuwa.
Hukumar Wutar lantarki ta Abuja zata yankewa hedikwatar Sojoji dana ‘yansanda wuta saboda bashi

Hukumar Wutar lantarki ta Abuja zata yankewa hedikwatar Sojoji dana ‘yansanda wuta saboda bashi

Siyasa
Hukumar wutar lantarki ta Abuja ta bayyana cewa, zata yankewa manyan ma'aikatu da yawa wuta saboda bashin kudin wutar da ake binsu. Ta bayyana cewa, daga cikin hukumin da ake bin bashin akwai hukumar sojojin, dana 'yansanda da ma'aikatar mata ta tarayya, da jihar Kogi, da ma'aikatar Ilimi, da ma'aikatar masana'antu. Hukumar tace ba wata ma'aikata da zata dagawa kafa zata yanke mata wuta. Hakan na kunshene a cikin sanarwar da hukumar wutar ta fitar.
Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce ya yi niyyar ɗaukar sojoji milyan ɗaya da ƴan sanda milyan ɗaya da a ce ya zama shugaban Najeriya a zaɓen 2023

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce ya yi niyyar ɗaukar sojoji milyan ɗaya da ƴan sanda milyan ɗaya da a ce ya zama shugaban Najeriya a zaɓen 2023

Kano, Rabiu Musa Kwankwaso
Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce ya yi niyyar ɗaukar sojoji milyan ɗaya da ƴan sanda milyan ɗaya da a ce ya zama shugaban Najeriya a zaɓen 2023 Ɗan takarar shugaban ƙasar na jam'iyyar NNPP a zaɓén na 2023 da ya gabata, Engr Rabi'u Musa Kwankwaso ya furta hakan a hirarsa da BBC Hausa, ya ce wannan matakin zai inganta harkokin tsaron Najeriya da ya tabarbare a wasu sassan ƙasar. Wane fata zaku yi masa?
Mugunta ko cin Amana? Ji yanda shugaban wani kauye a jihar Katsina ya karbi cin hancin Naira dubu dari bakwai(700,000) ya amince aka kaiwa mutanen kauyensa hari har aka kash-she 30

Mugunta ko cin Amana? Ji yanda shugaban wani kauye a jihar Katsina ya karbi cin hancin Naira dubu dari bakwai(700,000) ya amince aka kaiwa mutanen kauyensa hari har aka kash-she 30

Katsina, Tsaro
Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Umar Dikko Radda ya bayyana yanda wani shugaban kauye ya karbi Naira dubu dari bakwai ya amince aka kai hari akan kauyenshi wanda yayi sanadiyyar kisan mutane 30. Gwamnan yace an samu hakanne a Guga dake Bakori. Ya kara da cewa ba zasu kyale ko wanene aka samu da hannu a harkar 'yan Bindigar ba. Saboda rayuwar mutanen jihar tafi ta mutum daya ko wanene shi.
Kan mu ya daure, Bamu san wanne hukunci zamu yi amfani dashi ba>>Hukumar ‘yansandan jihar Kano bayan da aka aika mata hukunce-hukuncen kotu har 5 da suka shafi masarautar Kano, saidai ta bayyana abinda zata yi nan gaba

Kan mu ya daure, Bamu san wanne hukunci zamu yi amfani dashi ba>>Hukumar ‘yansandan jihar Kano bayan da aka aika mata hukunce-hukuncen kotu har 5 da suka shafi masarautar Kano, saidai ta bayyana abinda zata yi nan gaba

Kano, Siyasa
Hukumar 'yansandan jihar Kano ta bayyana tsaka mai wuya da take ciki kan hukunce-hukuncen kotu har guda biyar da aka yi kan masarautar Kano. Kwamishinan 'yansandan jihar, Mr Usaini Gumel ne ya bayyanawa manema labarai hakan inda yace sun tattara duka wadannan hukunce-hukuncen 5 sun aikewa da shugaban 'yansanda na kasa yayin da shi kuma ya aikawa da ministan shari'a. Yace suna jiran ministan shari'ar ya gaya musu da wane hukunci zasu yi amfani. Yace da zarar sun samu umarni daga ministan shari'ar, zasu zartas da hukuncin da doka ta amince dashi. Yayi kira kan kafafen yada labarai da su rika tantance labari kamin su yadashi.
An soki Peter Obi saboda kiran ‘yan Bindigar Arewa ‘yan Ta’dda amma yaki kiran ‘yan IPOB da ‘yan ta’adda

An soki Peter Obi saboda kiran ‘yan Bindigar Arewa ‘yan Ta’dda amma yaki kiran ‘yan IPOB da ‘yan ta’adda

Siyasa
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2023, Peter Obi ya yi Allah wadai da harin da 'yan IPOB suka kai da ya kashe sojoji 5 a jihar Abia. A baya dai, an yi tsammanin ba zai yi magana akan lamarin ba saidai yazo yayi maganar. Amma kuma ya kaucewa kiran 'yan IPOB din da 'yan ta'adda. Tsohon hadimin Shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad ne ya bayyana hakan inda ya dauko wani tsohon sakon na Peter Obi wanda yayi magana akan wani hari da aka kai jihar Filato inda ya kira maharan da sunan 'yan ta'adda. https://twitter.com/BashirAhmaad/status/1796877604475040183?t=ynvg3_I3Mpo8KjuxyO6U9w&s=19 A zamanin mulkin shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne dai aka ayyana kungiyar ta IPOB dake ikirarin kafa kasar Biafra da sunan kungiyar ta'ddanci.