Wednesday, February 18
Shadow

Duk Labarai

A yi rawa me tsafta sannan kada a Sha Gyìyà>>Shugaba Tinubu ya gayawa Kiristoci masu Bikin Kirsimeti

A yi rawa me tsafta sannan kada a Sha Gyìyà>>Shugaba Tinubu ya gayawa Kiristoci masu Bikin Kirsimeti

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bukaci 'yan Najeriya Kiristoci da su yi bikin Kirsimeti me tsafta. Sannan yayi kira a garesu da kada su sha giya sannan a yi rawa me tsafta. Sannan yace kada a tsokani fada. Shugaban ya bayyana hakane a Legas inda yake hutun Kirsimeti. https://twitter.com/NigeriaStories/status/2002867226463084805?t=OQ9h_u8_HVZMjBTimdQllg&s=19
Da Duminsa: FIFA tace ta karbi Korafin Najeriya akan Dr. Congo kuma tana bincike akai

Da Duminsa: FIFA tace ta karbi Korafin Najeriya akan Dr. Congo kuma tana bincike akai

Duk Labarai
Rahotanni da muke samu a yanzu haka na cewa, Hukumar kwallon kafa ta Duniya, FIFA ta karbi korafin Najeriya akan Dr. Congo kuma tace tana bincike akan lamarin. Najeriya ta shigar da korafin cewa, kasar Dr. Congo ta yi amfani da 'yan wasa masu kasashe biyu a wasan da suka buga da Najeriya wanda hakan ya sabawa dokar kasar. Idan Najeriya ta yi nasara a wannan Shari'ar, akwai yiyuwar zata buga gasar cin kofin Duniya na shekarar 2026.
Da Duminsa:’Yansanda sun mamaye Otal din Azir da Azir Arena mallakin Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami dake tsare a hannun EFCC

Da Duminsa:’Yansanda sun mamaye Otal din Azir da Azir Arena mallakin Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami dake tsare a hannun EFCC

Duk Labarai
Rahotanni sun ce an ga 'yansanda sun mamaye Otal din Azir da Azir Arena dake jihar Sakkwato wanda mallakin tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami ne. Malami dai yana hannun hukumar EFCC tana bincikensa. Ana zarginsa da Almundahanar kudade masu yawa. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2002726485363470604?t=8ZQ3Nvma9rAUyTnPU9_1YA&s=19
Kalli Bidiyon: Na je wata makarantar Allo, nawa Malaminsu Albashin Naira dubu 50 duk wata>>Inji Peter Obi

Kalli Bidiyon: Na je wata makarantar Allo, nawa Malaminsu Albashin Naira dubu 50 duk wata>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa, na jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2023, Peter Obi ya bayyana cewa, ya je wasu makarantun Allo inda ya tambayi nawa ake biyan malaman? Yace Ya yiwa malaman Albashin Naira 50,000. Sannan kuma ya dauki malaman koyar da Turanci da Lissafi da kimiyya da fasaha suma ya musu Albashin Naira dubu 50,000. Ya bayyana cewa, yana da yakinin yaran zasu sama masu amfani anan gaba. https://twitter.com/dammiedammie35/status/2002659483143831905?t=jl551SBr27lgrN2dqstf6w&s=19