
Malamin Jami’ar da ake zargi ya nemi matar aure a Kano har aka masa na jaki ya fito ya bayyana bangarensa abinda ya faru.
Malamin yace wallahi sharri aka masa bai yi lalata da matar ba.
Yace asalima itace ta bayyana masa cewa, wai su je su yi soyayyar Ice Cream.
Yace har turanci ta masa duk da shi malami ne amma bai taba jin irin wannan Turancin ba.
Yace itace ta gaya masa cewa su je wani gidan cin abinci amma yaki yadda yaje.
Malamin ya kara da cewa Allah ya taimaka a cikin BUK ne abin ya faru wajene na masu ilimi amma da a wajene Allah kadai yasan me za’a masa.