Friday, July 17
Shadow

Da gangan Tinubu ya jefa ‘yan Najeriya cikin Yunwa, kuma irin yanda ake kulle dashi ko dansa Seyi sai baiwa shugaban hukumar zabe INEC ba zai ci zaben shekarar 2027 ba>>Inji Solomon Dalung

Tsohon Ministan matasa sa wasanni, Solomon Dalung ya bayyana cewa ko da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dansa Seyi zai baiwa shugaban hukumar zaben me zaman kanta INEC ba zai ci zaben shekarar 2027 ba.

Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan jaridar Sunnews.

Yace Tinubu ya ja dagar yaki da mutanen Najeriya saboda jefasu a halin yunwa da yayi wanda ba’a taba samun irin hakan ba a tarihin Najeriya.

Dalung yace ko da tururuwar da ake ta shiga APC ba wai dan farin jinin shugaba Tinubu bane, ana yi ne saboda kare muradun siyasa da kuma tsoron kamu.

Karanta Wannan  Ina Son In Sanar Al'ummar Jihar Katsina Da Ku Cewar "Shugaban Kasa Bola Tinubu Zai Zo Jihar Katsina Kuma Ya Kwana, Wanda Bai Taɓa Yi Ba A Cikin Jihohin Najeriya, Bayan Mahaifarsa Jihar Legas, Domin Taya Mu Murna Da Kuma Ƙaddamar Da Ayyuka. Ina Kira Ga Al'ummar Jihar Katsina Su Fito Tarbar Shugaban Kasa".

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *