Monday, August 10
Shadow

Gwamnatin tarayya ta fara gyaran manyan Tituna a duk fadin Najeriya

A shirye-shiryen bukukuwan karshen shekara, Gwamnatin tarayya ta fara gyaran manyan titunan kasarnan.

Hukumar dake kula da titunan Najeriya, FERMA ce dai ta ke kula da gyaran.

Shugaban hukumar, Engr. Chukwuemeka Agbasi ne ya kaddamar da fara gyaran titunan a jihar Kano.

Yace za’a yi wadannan kyaran ne dan samarwa mutane saukin ziyara da komawa garuruwansu dan yin bukukuwan karshen shekara.

Yace sun gano titunan da aka fi amfani dasu kuma sune zasu fi baiwa fifiko a wajan gyaran.

Ya bayyana cewa, wannan aiki zai samarwa da mutane akalla 12,000 abin yi wanda hakan zai habaka tattalin arzikin kasa.

Karanta Wannan  Na yi aiki da mata kyawawa masu yawa babu wadda ta taba cewa na nemeta sai Sanata Natasha Akpoti, dadin abin ba ni kadai ta taba kalawa sharri ba>>Sanata Godswill Akpabio

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *