Saturday, August 8
Shadow

Idan Kun saci kudin Talakawa ku daina kaiwa kasashen Turawa>>Dangote ya baiwa barayin Gwamnati a Najeriya shawara

Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa bai kamata ace masu satar kudin talakawa suna kai kudaden kasashen turawa ba.

Dangote yace babu kasar da ba’a sata, amma banbancin misalin kasashen Asia dana Afrika shine, idan sun saci kudin suna zuba jari dasu ne a kasashen su maimakon kaiwa kasashen Turawa.

Dangote yace ba wai yana karfafawa jami’an gwamnati satar kudin talakawa bane amma yana da kyau su san cewa kamata yayi su rika amfani da kudin a cikin gida maimakon kaiwa kasar waje dan ci gaban kasar.

Karanta Wannan  Fadar shugaban kasa tace ba zata yafewa Peter Obi ba saboda cewar da yayi da shine shugaban kasa zai amince Amirka ta kawo Khari Najeriya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *