
Tauraron fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya fito ya bayyana dalilin da yasa ya saki matarsa Maimuna.
Adam ya bayyana a shafinsa na Instagram cewa, Sun gano suna da kwayoyin halitta iri daya shi da matarsa watau A.A shiyasa suka rabu.
Saidai Adam A. Zango yace bayan wannan babu wata rashin jituwa a tsakaninsu inda ya wallafa Bidiyon lokacin da Maimuna ke barin gidansa, yace ta bar gidansa tana cikin farin ciki.