
Wasu mutanen daji da suka dauki wasu dattawa 2 suka kuma fitar da Bidiyon su suna rokon a karbosu sun dauki hankula.
Da yawa dai sun bayyana alhini inda suka wa dattawan fatan Allah ya kubutar dasu.
Bayan fitar Bidiyon, an gano daya daga cikin mutanen dake hannun mutanen dajin shugaban jam’iyyar APC ne a garin koko dake karamar hukumar Besse ta jihar Kebbi.