
A jiyane dai muka kawo muku rahoton cewa, babban malamin Addinin Islama dake Kaduna, Sheikh Tukur Almanar na rigima da wata mata akan fili.
Matar har ta kaishi Brekete family.
Da farko da aka kirashi ya bayyana cewa, ba zai yi magana ba, zai aika Lauyansa.
Saidai daga baya, Ordinary President Ahmad Isa ya bayyana cewa, Malam yace ya barwa matar Filin.
Sannan ya bayar da kudi tallafi gareta dan ta fara ginin.