Friday, July 17
Shadow

Kwankwaso ba zai yi nasara a zaben 2027 a Kano ba>>Inji Ganduje

Shugaban Jam’iyyar APC ta kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa, Mutanen Kano ba zasu sake goyawa Kwankwaso baya ba.

Yace ko da a 2023 ma rikicin cikin gida na Jam’iyyar APC ne yasa Kwankwaso yayi nasara a zaben, yace amma wanda suka zabi Jam’iyyarsa ta NNPP a yanzu suna nadama.

Ya bayyana hakane a wajan taron karrama jiga-jigan Jam’iyyar da aka yi inda shugaban APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas ya wakilceshi.

Ganduje yace yakan yi mamaki idan yaji Kwankwaso na cewa yana da goyon bayan mutanen jihar, yace gashinan Gwamna Abba Kabir Yusuf ma duk a rude yake bai san abinda ke tafiya a gwamnatinsa ba.

Karanta Wannan  Majalisar mu ta dattijai kamar kungiyar tsafi take, kowane Sanata na tsoron ya soki kakakin majalisa, Akpabio ya taba rike min hannu ya rika murzawa, kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi>>Sanata Natasha Akpoti ta sake yiwa Akpabio tonon silili

Ganduje yayi kira ga ‘yan Jam’iyyar ta APC da su hada kansu inda yace ta hanyar hakane musamman zasu samu nasarar kwace Jiyar daga hannun NNPP.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *