Saturday, December 13
Shadow
Matatar Dangote ta kara farashin man fetur

Matatar Dangote ta kara farashin man fetur

Duk Labarai
Matatar Man fetur din Dangote ta kara farashin man fetur dinta a gidan man MRS dake Abuja zuwa Naira 950 akan kowace lita. Rahotanni sun ce ranar Talatar data gabata, Gidan man na MRS dake Abuja na sayar da man sa akan Naira 851 kan kowace lita amma zuwa ranar Laraba sai aka ga sun canja farashi zuwa 950. Hakanan sauran gidajen man dake da alaka da Dangote irin su Ardova da Optima suma sun canja Farashin nasu zuwa sama. Daya daga cikin manajojin gidan man MRS ya shaidawa kafar Daily Post cewa, matatar man Dangote ta kara farashin da take sayarwa da 'yan kasuwa man.
Ana rade-radin cewa, Gwamnati ta soke Jarabawar JAMB, Gwamnatin ta yi martani

Ana rade-radin cewa, Gwamnati ta soke Jarabawar JAMB, Gwamnatin ta yi martani

Duk Labarai
Rahotanni sun watsu sosai cewa, Gwamnatin Tarayya ta soke jarabawar JAMB a matsayin ma'unin shiga jami'a. Saidai a martanin Gwamnatin ta bakin ministan Ilimi, Dr. Maruf Tunji Alausa CON, yace wannan labari ba gaskiya bane kuma ba daga hannunsu ya fito ba. Yace domin kawar da duk wata tantama, JAMB har yanzu itace jarabawar da dalibai zasu rika yi dam samun damar shiga jami'a. Yace kuma zasu ci gaba da hada kai da JAMB dan cimma burikan Ilimi.
Kalli Bidiyon: Ba kudi aka bani na yi ridda na koma Kirista ba, yanzu abu daya nake nema wajan Malaman Musulmai shine su nuna min inda aka cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi Sallah sau biyar a rana a cikin Qur’ani>>Inji Abubakar dan jihar Borno da yayi Ridda

Kalli Bidiyon: Ba kudi aka bani na yi ridda na koma Kirista ba, yanzu abu daya nake nema wajan Malaman Musulmai shine su nuna min inda aka cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi Sallah sau biyar a rana a cikin Qur’ani>>Inji Abubakar dan jihar Borno da yayi Ridda

Duk Labarai
Matashi Abubakar dan jihar Borno wanda yayi ridda ya koma Kirista ya bayyana cewa, ba gaskiya bane labarin da ake yadawa cewa kudi aka bashi ya koma kirista. Yace bincikene yayi ya gano gaskiya. Yace yanzu abinda yake so shine a samu malamai su nuna masa inda aka cewa, Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi sallah sau biyar a Qur'ani. Yace idan aka nuna masa zai sake komawa Musulunci. https://www.tiktok.com/@winningsoulsminist/video/7561786035257068818?_t=ZS-90cR6JKMTA1&_r=1
Kalli Bidiyon:Munji Dadin Abinda Kwamitin Shura na Kano suka yi game da Malam Lawal Triumph, Yanzu muna jiransu su kira wadanda suka cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Raqumi da Hankaka suma su kawo hujja a litattafan da suka samo hakan>>Inji Shugaban Izala, Sheikh Bala Lau

Kalli Bidiyon:Munji Dadin Abinda Kwamitin Shura na Kano suka yi game da Malam Lawal Triumph, Yanzu muna jiransu su kira wadanda suka cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Raqumi da Hankaka suma su kawo hujja a litattafan da suka samo hakan>>Inji Shugaban Izala, Sheikh Bala Lau

Duk Labarai
Shugaban Izala, Sheikh Bala Lau yace sun ji dadin Abinda Kwamitin Shura na Kano suka yi akan malam Lawal Triumph. Yace sun jinjina musu, yace amma kuma suna jiran su ga an gayyaci wadanda suka kira Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da Raqumi da kuma hankaka, kamar yanda malam Lawal Triumph ya bude littafi ya kawo hujja, suma su bude littafi su kawo Hujjar inda suka ga hakan. Yace idan kuwa ba a yi hakan ba to ba'awa Ahlussunah Adalci ba. https://www.tiktok.com/@taskarmalanlawantriumph/video/7561563264598035719?_t=ZS-90cQ5985Fx3&_r=1
Akwai yiyuwar Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai fasa yafewa Maryam Sanda bayan da cece-kuce yayi yawa akan yafiyar da aka ma

Akwai yiyuwar Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai fasa yafewa Maryam Sanda bayan da cece-kuce yayi yawa akan yafiyar da aka ma

Duk Labarai
Rahotanni sun ce akwai yiyuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai canja ra'ayi kan yafiyar da yawa wasu masu laifi dake tsare a gidajen yarin kasarnan. Yafiyar shugaban kasa ga masu laifi ana yintane dan rage cinkoso a gidajen yari musamman ga masu laifin da ake ganin bashi da tsauri sosai. Saidai bayan fitowar Jadawalin masu laifin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yafewa an ta cece-kuce musamman saboda ganin wasu sunayen manyan masu laifi da ake ganin bai kamata a yafe musu ba saboda munin laifukan da suka aikata. Babban lauyan Gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi (SAN) ya bayyana cewa, har yanzu ba'a kammala yafewa masu laifin ba, ana kan sake dunaba sunayen wadanda akawa yafiyar, inda yace bayan nan ne za'a gabatarwa da hukumar kula da gidajen yarin kasarnan dan a saki wad...
Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Naija ya jawo cece-kuce sosai bayan da aka ganshi ya shiga coci an yi irin addu’ar kiristoci dashi

Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Naija ya jawo cece-kuce sosai bayan da aka ganshi ya shiga coci an yi irin addu’ar kiristoci dashi

Duk Labarai
Gwamnan jihar Naija, Umar Bago ya jawo cece-kuce sosai bayan da aka ganshi a coci yana wakoki da addu'o'i irin na kirista. Gwamman ya shiga cocin Living Faith Church ne dan yin Addu'ar zaman lafiya. Wasu dai musamman 'yan Kudu sun rika cewa da talaka ne da watakila an dauki mataki akanshi. https://twitter.com/dammiedammie35/status/1978900420727611692?t=opFPHjWvCYxCu8By6niDvA&s=19
Me Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar II ya nemi Gwamnati ta yi dokar sanya ido a kafafen sadarwa saboda chin Mutuncin da ake yiwa manyan mutane yayi yawa

Me Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar II ya nemi Gwamnati ta yi dokar sanya ido a kafafen sadarwa saboda chin Mutuncin da ake yiwa manyan mutane yayi yawa

Duk Labarai
Me Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III ya nemi Gwamnati data yi sabuwar dokar da zata rika saka ido a kafafen sada zumunta saboda cin fuskar da akewa manyan mutane ta yi yawa. Hakanan ya bayyana cewa ana amfani da kafafen sada zumuntar dan barazanar tsaro. Yace amfani da kafafen sadarwa ta hanyar da bata kamata ba na barazana ga zaman lafiya, Girmama juna, da hadin kan kasarnan. Ya bayyana hakane ta bakin Me martaba sarkin Zazzau, Ahmad Nuhu Bamalli a wajan taron manyan malamai daya gudana a Kaduna wanda aka yi saboda tattauna matsalar tsaro da zaman takewa. Yace a wasu kasashen akwai dokar amfani da kafafen sadarwa ta yanda idan mutum ya saka sakon da bai kamata ba ko na cin zarafi za'a nemoshi a hukuntashi. Yayi kira ga mahukunta dasu dauki irin wannan mata...
Lura da irin Arzikin da Allah yawa Najeriya, bai kamata akwai talaka a kasarnan ba>>Inji Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Lura da irin Arzikin da Allah yawa Najeriya, bai kamata akwai talaka a kasarnan ba>>Inji Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, Lura da irin Arzikin ma'adanan karkashin kasa da Allah yawa kasarnan, bai kamata ace akwai talaka a kasarba Shugabab ya bayyana hakane a wajan taro kan Arzikin ma'danan karkashin kasa da Allah yawa Najeriya da ya gudana a Abuja. Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume ne ya wakilci shugaban kasar a wajan taron. Ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya zata yi dukkan mai yiyuwa wajan samar da yanayi me kyau na zuba hannun jari a kasarnan ta bangaren ma'adanan karkashin kasa. Sannan ya yi kira ga kasashen Afrika dasu yi amfani da ma'adannan karkashin kasar da Allah ya hore musu dan karfafa tattalin arzikin su.