Thursday, December 18
Shadow
Masu shirin Yin Zqngq-Zqnzqr neman a Saki Nnqmd1 Kqnu sun ce ba gudu ba ja da baya duk da gargadin jami’an tsaro

Masu shirin Yin Zqngq-Zqnzqr neman a Saki Nnqmd1 Kqnu sun ce ba gudu ba ja da baya duk da gargadin jami’an tsaro

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, masu shirya zanga-zangar neman a saki shugaban Haramtacciyar kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu a yau Litinin, Sun ce ba gudu ba ja da baya duk da gargadin da jami'an tsaro suka musu. Masu zanga-zangar sun shirya yin tattaki zuwa fadar shugaban kasa dan neman a saki Nnamdi Kanu. Hakan kuma na zuwane a yayin da Babbar kotun gwamnatin tarayya ta hana masu zanga-zangar zuwa kusa da fadar gwamnati ko kuma kuma majalisar tarayya ko duk wani ginin gwamnati. Saidai duk da wannan, masu zanga-zangar sun ce ba gudu ba ja da baya, hakanan shugaban Zanga-zangar, Omoyele Sowore yace maganar umarnin Kotun ba gaskiya bane. Idan dai masu zanga-zangar suka fito, akwai yiyuwar za'a yi dauki ba dadi tsakaninsu da jami'an tsaro.
Kalli Bidiyon: Ba wanda zai hanani ci gaba da Yin tik din Muslim Muslim na Tinubu da Kashim Shettima, kaima ban hanaka yin naka ba>>Sheikh Sani Yahya Jingir

Kalli Bidiyon: Ba wanda zai hanani ci gaba da Yin tik din Muslim Muslim na Tinubu da Kashim Shettima, kaima ban hanaka yin naka ba>>Sheikh Sani Yahya Jingir

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Sani Yahya Jingir ya bayyana cewa, Ba zai daina son Tikitin takarar shugaban kasa na Muslim Muslim ba. Yace ba dan kowa yake yi ba sai don Allah. Malam yace bai hana kowa yin nashi ba amma kuma shima babu wanda zai hanashi yin nashi. https://www.tiktok.com/@i_am_saeed01/video/7562482931617336588?_t=ZS-90gKuhqfIoK&_r=1
Kalli Bidiyo: Na bar Shirka da Kafurcin Dariqa, daga yau na fita daga Dariqa>>Inji Abu Hanifa

Kalli Bidiyo: Na bar Shirka da Kafurcin Dariqa, daga yau na fita daga Dariqa>>Inji Abu Hanifa

Duk Labarai
Wani dan Dariqa da ake kira da Abu Hanifa ya bayyana cewa ya bar Dariqar. Yace ya bar Shirka da Kafirci inda yace ba dama mutum ya ga ba daidai ba yayi magana sai a rika kiransa da munafiki. Ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa da ya wallafa a shafinsa na Tik. https://www.tiktok.com/@sanusi.umar18/video/7562128044677287169?_t=ZS-90g75j8pRZY&_r=1
Gwamnatin Kano ta rufe wajan shan Shyshaa me suna ARAFAT

Gwamnatin Kano ta rufe wajan shan Shyshaa me suna ARAFAT

Duk Labarai
iGwamnatin jihar Kano ta rufe wajan shan shisha me suna Arfat Shisha Lounge Hukumar kula da yawon shakatawa ta jihar hadi da hukumar yaki da shan miyagun kwayoyi, NDLEA ne suka rufe wajan shan shishar. Shugaban hukumar shakatawar Alhaji Tukur Bala Sagagi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa inda yace wannan kokari ne na kawar da ayyukan ta'ammuli da miyagun kwayoyi a jihar. Yace a jihar ta Kano, Akwai dokar Haramta shan Shisha kuma zasu ci gaba da karfafa wannan doka.
Wani Magidanci ya je ofishin ‘yansanda na jihar Kano inda yace zai kara aurene shine ya baiwa matarsa Naira Miliyan 2 toshiyar baki, shine yake neman shawara ko hakan ya sabawa doka?

Wani Magidanci ya je ofishin ‘yansanda na jihar Kano inda yace zai kara aurene shine ya baiwa matarsa Naira Miliyan 2 toshiyar baki, shine yake neman shawara ko hakan ya sabawa doka?

Duk Labarai
Wani magidanci ya je ofishin 'yansanda na jihar Kano inda yace zai kara aurene dan haka ya baiwa matarsa toshiyar baki ta Naira Miliyan 2. Shine yake neman shawara ko hakan ya dace da doka? Kakakin 'yansandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya wallafa labarin a shafinsa na Facebook.
Kalli Bidiyon yanda aka shirya yakin neman zabe a Legas dan kira ga Shugaba Tinubu ya fito takara a 2027

Kalli Bidiyon yanda aka shirya yakin neman zabe a Legas dan kira ga Shugaba Tinubu ya fito takara a 2027

Duk Labarai
Mutane da yawa ne a Legas suka fito dan kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sake fitowa takara a shekarar 2027. An ga mutanen na daga kwalaye masu dauke da hotunan shugaban kasar. Saidai wasu sun yi zargin an baiwa mutanen kudi ne. Hakanan hukumar zabe me zaman kanta INEC a hana irin wannan yakin neman zabe tun kamin lokacin zabe yayi. https://twitter.com/GossipMillNaija/status/1979661716872216952?t=7guCszb453jpOzWzCHCLGg&s=19
Babban Sojan Najeriya Lt. Col. Aliyu Saidu Paiko da wasu sojoji 5 dake tare dashi sun rigamu gidan gaskiya a fagen daga a jihar Borno

Babban Sojan Najeriya Lt. Col. Aliyu Saidu Paiko da wasu sojoji 5 dake tare dashi sun rigamu gidan gaskiya a fagen daga a jihar Borno

Duk Labarai
Sojan Najeriya, Lt. Col. Aliyu Saidu Paiko da wasu sojoji 5 sun rigamu gidan gaskiya a jihar Borno a yayin da aka kai musu Harin Kwantan Bauna. Lamarin ya farune ranar 17 ga watan October 2025 inda kuma aka kashe CJTF 3. https://twitter.com/Edrees4P/status/1979681137967690102?t=BsJtahuOK0wLPAnT2ZDUVA&s=19
Muma Mun samu bayanan cewa lallai an shirya yiwa Shugaba Tinubu Juyin Mulki, kuma Sojojin da aka kama dalilin haka suna da yawa>>Inji Jaridar Punchng

Muma Mun samu bayanan cewa lallai an shirya yiwa Shugaba Tinubu Juyin Mulki, kuma Sojojin da aka kama dalilin haka suna da yawa>>Inji Jaridar Punchng

Duk Labarai
Jaridar Punchng ta zama ta uku kenan data ruwaito cewa, an kama wasu sojoji da suka shirya yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki. Jaridar tace wata majiyar soji ta tabbatar mata da cewa kamen da kawa wasu sojoji sama da 16 na da alaka da shirin juyin Mulkin da suke shirin yiwa Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Jaridar Punchng ta kara da cewa wani janar ne ka jagoranar sojojin da ke shirin kifar da Gwamnatin Shugaba Tinubu wanda suka shirya yi ranar 1 ga watan October. Saidai Hukumar sojojin Najeriya ta ce karyane babu wani shirin jurin mulki aka yiwa shugaba Tinubu. Jaridar Sahara reporters ce ta fara kawo labarin tace an kama sojoji 16 inda daga baya Premium times itama ta ce ta samu wanan rahoto inda tace an kama sojoji 20. Rahoton jaridar Punchng yace amma k...