Saturday, December 13
Shadow
Na yadda da Mukabalar ‘yan Izala amma a Turomin Guruntum ko Sheikh Sani Rijiyar Lemu saboda ina son babban dan Izala ne wanda idan na mai Kwaf daya na gama da Izala>>Inji Malam Abdulfatahi Sani Tijjani

Na yadda da Mukabalar ‘yan Izala amma a Turomin Guruntum ko Sheikh Sani Rijiyar Lemu saboda ina son babban dan Izala ne wanda idan na mai Kwaf daya na gama da Izala>>Inji Malam Abdulfatahi Sani Tijjani

Duk Labarai
Malam Abdulfatahi Sani Tijjani ya ce ya amince da gayyatar mukabala daga kungiyar Izala. Saidai yace ba zai zauna da kananan malamai ba. Yace a tura masa ko dai Guruntum ko kuma Sheikh Sani Rijiyar Lemu, yace yana son wadanda idan ya doke su asan ya doke Izala. Yace kamar yanda suka buga da marigayi Sheikh Idris Dutsen Tanshi ya dokeshi haka yake son sake bugawa da wani babban malamin Izala shima ya gama dashi. https://www.tiktok.com/@habibou.adamou..227/video/7557329579254254904?_t=ZS-90IzP4iQzzN&_r=1
Duk Duniya ba garin da nake so sama da Kano amma ba zan iya zama a Kano ba, Mai Wushirya yana can an kamashi saboda yawa Wada Khyss>>Inji G-Fresh Al-amin

Duk Duniya ba garin da nake so sama da Kano amma ba zan iya zama a Kano ba, Mai Wushirya yana can an kamashi saboda yawa Wada Khyss>>Inji G-Fresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, G-Fresh Al-amin ya bayyana cewa, duk Duniya ba garin da yake so fiye da Kano amma Kano ba zata zauno masa ba. Ya bayyana hakane inda ake bayar da misali da kamen da kawa Mai Wushirya. G-Fresh yace Mai Wushirya na can a hannu bayan da yawa Gurguwa Kiss. Ya kuma saka Bidiyon Soja Boy da yake cewa Babu malamin da zai halasta maka rawa da waka. Inda G-Fresh yace Nishadantarwa kawai suke. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7557472377332960530?_t=ZS-90IyDWhwPhJ&_r=1
Gwamnatin Jihar Kano zata sake aurar da Zawarawa akan Naira Biliyan 1

Gwamnatin Jihar Kano zata sake aurar da Zawarawa akan Naira Biliyan 1

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya amince da kashe Naira Biliyan 1 da Miliyan 6, domin auren zawarawa karo na biyu. Kwamishin yaɗa labarai da harkokin cikin gida Kwamarad Ibrahim Abdullahi Waiya ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da manema labarai kan sakamakon zaman majalisar zartaswar jihar Karo na 32 da ka gudanar ranar juma'ar da ta gabata. Me zaku ce?
Muna nan akan Bakanmu, kowa sai ya biya Haraji, ko ta hanyar halarar ya samu kuri ko bata ta hanyar halal ba, Qaruwai, Kwandastan Mota, dama kowace irin sana’a kake nan da 2026 sai ka fara biyan Haraji>>Inji Gwamnatin Tinubu

Muna nan akan Bakanmu, kowa sai ya biya Haraji, ko ta hanyar halarar ya samu kuri ko bata ta hanyar halal ba, Qaruwai, Kwandastan Mota, dama kowace irin sana’a kake nan da 2026 sai ka fara biyan Haraji>>Inji Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, tana nan akan bakanta na cewa, kowa sai ya biya haraji. Shugaban kwamitin Gyaran fasalin kudi na shugaban kasa, Taiwo Oyedele ne ya bayyana haka a wata ganawa da manema labarai. Yace a Duniya gaba daya haka tsarin yake, ko ta wace hanya ka samu kudi sai ka biya Haraji, yace idan ance wanda suka samu kudi ta hanyar Halal ne kadai zasu biya haraji, to sai wasu su koma samun kudi ta hanyar Haram dan su kaucewa biyan Harajin. Yace hukumar karbar Haraji ta kasar Amurka nada taken cewa ko sata kayi sai ka biya Haraji.
Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan na shirin komawa jam’iyyar ADC

Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan na shirin komawa jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan na shirin komawa jam'iyyar ADC. Wasu majiyoyi ne suka fadawa kafar Punchng hakan a asirce daga jam'iyyar ADC din saboda basu da ikon yin magana da yawun jam'iyyar. An jima dai ana rade-radin cewa, tsohon shugaban kasar zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 amma shi bai fito ya tabbatar da hakan a hukumance ba.
Allah ya kawo mu zamanin Wawaye da Jahilai kowa sai fadin abinda yaga dama akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yake>>Inji Sheikh Umar Sani Fage

Allah ya kawo mu zamanin Wawaye da Jahilai kowa sai fadin abinda yaga dama akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yake>>Inji Sheikh Umar Sani Fage

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Umar Sani Fagge ya yi raddi sosai akan masu yin kalamai da basu dace ba akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Malam yace idan aka samu mutum da laifi zai iya kaiwa a dauki hukuncin khisa akansa. https://www.tiktok.com/@mai.6013/video/7557485955301625095?_t=ZS-90I9Vj3gtdp&_r=1