Monday, December 15
Shadow
Ji yanda aka kama wani Barawon waya da ya sace wayar wata mata tana bacci amma bai kashe wayar ba, data kira yace sai ta bashi dubu 50

Ji yanda aka kama wani Barawon waya da ya sace wayar wata mata tana bacci amma bai kashe wayar ba, data kira yace sai ta bashi dubu 50

Duk Labarai
Wani barawo ya sace wayar wata mata yayin da take tsaka da bacci. Saidai be kashe wayar ba. Da me wayar ta kira, sai yace zai bata amma sai ta bashi dubu hamsin. Saidai tace masa bata da Dubu 50. Amma tace idan yana so zata bashi kanta. Aikuwa sai ya yadda. Tuni dai an kamashi, lamarin ya farune a Ikotun, dake jihar Lagos. https://twitter.com/stilldey4u/status/1975825042433790433?t=BKJonJHQDeI_6w3vR9tCJg&s=19
Kalli Bidiyo: Ana ci gaba da daukar sabuwar wakar Soja Boy inda aka ga Bidiyo yana kama Khugun Iftihal Madaki wadda a baya aka saba ganinta da Hijabi

Kalli Bidiyo: Ana ci gaba da daukar sabuwar wakar Soja Boy inda aka ga Bidiyo yana kama Khugun Iftihal Madaki wadda a baya aka saba ganinta da Hijabi

Duk Labarai
Ana ci gaba da daukar Bidiyon sabuwar wakar Soja Boy wadda suka yi Bidiyon ta tare da iftihal Madaki wadda a baya aka saba ganinta sanye da Hijabi a Bidiyon ta. A Bidiyon an ga yanda Soja Boy ya kamo Kugun Iftihal yayin da take sanye da doguwar bakar Riga. A wakar da suka yi da ita ta farko, Iftihal ta jawo cece-kuce sosai bayan ganinta tana rawa ba Hijabi. https://www.tiktok.com/@bigdoxxx/video/7558599404547083536?_t=ZS-90NSeHnCzIX&_r=1
Kalli Bidiyo: Wasannan na Mari da ake ganin Turawa na yi ya shigo Najeriya

Kalli Bidiyo: Wasannan na Mari da ake ganin Turawa na yi ya shigo Najeriya

Duk Labarai
Wasan Mari da mafi yawanci ake ganin Turawa na yi ya shigo Najeriya. Wasan wanda har ana saka kyauta ga wanda yafi iya yin marin an ganshi an fara yinshi a Najeriya. Lamarin dai ya baiwa mutane mamaki sosai inda ake ta muhawara akai. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1975275774308663458?t=zMzci2-c8sk72ZCDflhcJw&s=19 Tuni dai wani malamin Addinin Islama ya jawo hankalin Musulmai da cewa wasan bai halasta ba a Musulunci kuma su gujeshi. https://twitter.com/IdrisAOni1/status/1975585618076774801?t=JQQfXTWH2WuPWr4dwZuinw&s=19
Kudi sun yi yawa a hannun mutane, Kuma na ji dadin matakan da CBN ya dauka wajan rage yawan kudaden dake hannun mutane>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Kudi sun yi yawa a hannun mutane, Kuma na ji dadin matakan da CBN ya dauka wajan rage yawan kudaden dake hannun mutane>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Duk Labarai
Me martaba sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya bayyana jin dadinsa game da matakan da babban bankin Najeriya CBN ya dauka wajan magance yawan kudi a hannun mutane. Sarki Sanusi yace hakan yasa hauhawar farashin kayan abinci ya ragu duk da dai har yanzu yana kan maki 20 wanda yayi yawa. Sarkin yace tattalin arzikin Najeriya ya dawo daga hanyar rugujewa da ya dauka saboda wanan mataki da CBN ya daka. https://twitter.com/KanEmirateMedia/status/1975645093714665940?t=wj0dZ4XwsPxOAD9AaX2o3A&s=19
Kalli Bidiyo: Wallahi da wadanda ba musulmai bane suka yi irin wannan Kalamai akan Janibin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da Musulmai sun turasu Qiyama>>Inji Farfesa Ibrahim Maqari

Kalli Bidiyo: Wallahi da wadanda ba musulmai bane suka yi irin wannan Kalamai akan Janibin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da Musulmai sun turasu Qiyama>>Inji Farfesa Ibrahim Maqari

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama Sheikh Farfesa Ibrahim Maqari Ya bayyana cewa, da wadanda ba musulmai bane suka yi kalamai na taba Janibin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yace da tuni hakan ya kawo tashin hankali. Malam yace "Da Tuni an fara Qone-Qone da an fhille Mhusu Khawuna. Yace amma wadanda suke kiran kansu musulmai ne ke irin wannan abin. Malam ya bayyana hakane cikin sheshekar kuka a wani Bidiyonsa da ya watsu sosai. https://www.tiktok.com/@hassan.a.hassan.2/video/7557739024941600011?_t=ZS-90N9J038S1p&_r=1
Ina mamakin yanda ake mana Qazafin wai muna Lalata da Mhata, Saboda matan dake bin mu mun yi ‘ya’ya da jikoki dasu>>Inji Tanimu Akawu

Ina mamakin yanda ake mana Qazafin wai muna Lalata da Mhata, Saboda matan dake bin mu mun yi ‘ya’ya da jikoki dasu>>Inji Tanimu Akawu

Duk Labarai
Tauraron Fina-finan Hausa, Tanimu akawu ya bayyana cewa, Abin na bashi mamaki wai da ake musu Qazafin cewa, suna lalata da mata. Yace yawanci matan dake binsu sun yi 'ya'ya da jikoki dasu. Yace dan fim me taimako ne inda yace shi kanshi ya aurar da yaran mutane 2. https://www.tiktok.com/@abdulsauty1/video/7558205933583617298?_t=ZS-90N7paOSItN&_r=1 Tanimu Akawu ya kawo misalin yanda wata yarinya bafulatana da akawa auren dole ta gudo ta sameshi tace tana son shiga film inda yace sai da ya kira iyayenta. Yace da Kano ta je da an lalata mata rayuwa.
”Yan Kasuwar Abuja na kokawa da Harajin da ake karba daga hannunsu saboda sauraren Radiyo da kallin TV

”Yan Kasuwar Abuja na kokawa da Harajin da ake karba daga hannunsu saboda sauraren Radiyo da kallin TV

Duk Labarai
'Yan kasuwar Abuja na kokawa da karbar Harajin Kallon TV da sauraren Radio da ake karba daga hannunsu. Daya daga cikin 'yan kasuwar ne ya wallafa Rasit din karbar Harajin. Ya koka da cewa, ta yaya za'a ce mutum ya biya Haraji saboda kallon Talabijin da Sauraren Radio? https://twitter.com/humeeemk/status/1975284134525259814?t=0k_zHhvRF9Clmaoa_5l-sQ&s=19