Hukumar kula da kididdiga ta kasa, NBS ta bayyana cewa, farashin kayan masarufi ya sauka sosai.
Hukumar ta bayyana hakane a cikin bayanan watan Nuwamba da ta fitar ranar Litinin a shafinta.
Tace idan ak kwatanta da shekarar data gabata, alkaluman farashin kayan Masarufin na kan maki 16.05 wanda kuma a yanzu suna kan makin 14.45.
Wasu rahotanni na jawo cewa, Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio ya yanke jiki ya fadi an garzaya dashi zuwa Asibiti.
Wata 'yar Jarida, Adeola Fayehun ce ta bayyana hakan.
Saidai zuwa yanzu ofishin Akpabio bai tabbatar ko karyata Rahoton ba
Tauraruwar fina-finan Hausa, Rashida Mai Sa'a wadda a kwanaki ta dauki hankula saboda kawo wani kwado da tace tana hana mazakutar mazan aure tashi idan aka kulleshi ta tabbatar da yin amfani da kwadon akan mijinta.
Wasu abokansu ne suka tsokane ta da hakan kuma bata musa ba.
A karshe sai aka ga sun kashe ita da mijinta.
https://www.tiktok.com/@hon.danbabangawuna/video/7583416702352755975?_t=ZS-92FE9qkOtYO&_r=1
Tauraruwar fina-finan Hausa, A'isha Soba tace a daina daukarta a cikin wani Bidiyo da aka ga ana daukarta ba ta yi Amfani da Filter ba.
Wasu dai sun ce duk da haka ta yi kyau.
https://www.tiktok.com/@ismailyaualolo/video/7583484036870475029?_t=ZS-92FDNygKzU9&_r=1
An ga taurarin Fina-finan Hausa Mata babu Filter a wani wajen da suka ziyarta.
An ga su Samha M. Inuwa, da Momi Gombe, da Amal Umar da sauransu duk da fuskokinsu na asli bau filter.
Da yawa dai sun bayyana mabanbanta ra'ayoyi kan Bidiyon.
https://www.tiktok.com/@realmahrazhamraz/video/7583413902952729864?_t=ZS-92FCi1PSBPt&_r=1
An zargi shugaban hukumar CAC dake wa kamfanoni Rijista, Magaji da saye gidan Dala $200,000 a kasar Morocco.
Yayi aure amma auren be dade ba ya lalace.
https://twitter.com/SaharaReporters/status/2000555225363689608?t=G9q6blnTG50tXxlB46pgWw&s=19
An hango Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi a masallaci.
Da yawa sun fassara hakan da cewa siyasar 2027 ce dake matsowa ta kaishi masallacin
https://twitter.com/General_Somto/status/2000490269532463114?t=bFwFjIhU-h0uJ9rIyQXBpg&s=19
Wani matashi da ya zana matar Rarara, A'ishatulhumaira ya dauki hankula.
Wasu sun yaba mai inda wasu suka kushe.
Saidai da yawa sun ce kada ya zana Rarara.
https://www.tiktok.com/@dear.mamah.art/video/7583626796495621397?_t=ZS-92F0xq8A76H&_r=1
Malam Dr. Hussain Kano ya sake tabbatar da maganarsa cewa baya son Allah ya kaishi matakin da sai ya nemi ceton Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) kamin ya shiga Aljannah ranar Qiyama.
Ya bayyana cewa masu sukarsa basu san Addini da kyau bane.
Yace aiki shine ke sanadin a saka mutum a Al-jannah amma mutum ya saki jiki yana sharholiya yana tunanin Manzon Allah SAW zai ceceshi ba daidai bane.
Yace duk wanda kaga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ceceshi to Fajirine, Ladarsa bata kai yawan da zata shigar dashi Aljannah ba.
https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7584025876900187403?_t=ZS-92EzKpE5PzE&_r=1