Tuesday, December 16
Shadow
Allah bai yi Duniya dan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba duk wanda yace Allah yayi Duniya dan Annabi karya yake>>Inji Malam Abdulrahman Umar

Allah bai yi Duniya dan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba duk wanda yace Allah yayi Duniya dan Annabi karya yake>>Inji Malam Abdulrahman Umar

Duk Labarai
Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah ya bayyana cewa, Allah bai yi Duniya dan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba. Malam yace Allah ya yi Duniya dan a Bauta masaa ne. Yace duk wanda yace Allah yayi Duniya dan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) karya yake. https://www.tiktok.com/@abdurrahmanumarr/video/7550806244898950421?_t=ZS-8znQ4uagzbt&_r=1
Kalli Bidiyon: Wani mutum da ya taba taimakon wannan matar da Naira dubu dari biyar da hamsin yayi mamakin ganinta tana bara da ‘ya’yanta akan titi

Kalli Bidiyon: Wani mutum da ya taba taimakon wannan matar da Naira dubu dari biyar da hamsin yayi mamakin ganinta tana bara da ‘ya’yanta akan titi

Duk Labarai
Wani mutuk yace ya taba taimakon wannan matar da Naira 550,000 amma abin mamaki shine sai gata ya ganta tana bara da 'ya'yanta akan titi. Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke cewa ko nawa mutum ke gareshi zasu iya karewa, wasu kuwa suna ganin akwai sakaci a lamarinta. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1967538943857189122?t=z1HGCNgOg_dZRzvWrWtAKA&s=19 https://www.youtube.com/watch?v=j0xF7esqXAY?si=AN7oY_9aWzkgHIjg
Soja Boy ya yi magana game da wannan hoton shi da Rahama Saidu a daki

Soja Boy ya yi magana game da wannan hoton shi da Rahama Saidu a daki

Duk Labarai
Tauraron mawakin Gambara me yawan amfani da kalaman batsa, wanda aka fi sani da Soja yayi martani bayan ganin wani hotonsa shi da Rahama Saidu a kan gado Hoton dai na AI wanda yayi ta yawo a kafafen sadarwa. Abin ya bashi dariya inda yace amma yanayin dakin ya burgeshi. Hakan na zuwane bayan da aka ga hotuna inda Soja Boy ya rungumi Rahama da kuma inda ya gaisa da ita.
Kalli Bidiyon: Mawaki 442 ya musuluntar da baturiyar da yakw waka da ita bayan da halayensa suka burgeta

Kalli Bidiyon: Mawaki 442 ya musuluntar da baturiyar da yakw waka da ita bayan da halayensa suka burgeta

Duk Labarai
Tauraron mawakin Gambara, 442 ya bayyana cewa baturiyar da aka ga suna waka tare da ita, ta karbi addinin Musulunci. Yace tana ganin yanda yake zuwa yana Sallah shine abin ya burgeta ta nuna masa sha'awar shiga Musulunci. Yace zai koyar da ita yanda zata bautawa Allah. https://www.tiktok.com/@mr442_/video/7550381377196150034?_t=ZS-8zmituSwmhd&_r=1
Ana ta surutu wai muna hada maza da mata a wajan Maulidi, to ba zamu daina hada maza da mata a wajan maulidi ba>>Inji Anisee

Ana ta surutu wai muna hada maza da mata a wajan Maulidi, to ba zamu daina hada maza da mata a wajan maulidi ba>>Inji Anisee

Duk Labarai
Shahararren dan darika, Masoyin Shehu Tijjani Alhaji Anisee ya bayyana cewa, ba zasu daina hada maza da mata a wajan Maulidi ba Ya bayyana hakane a matsayin raddi ga wani malamin darika da yace saboda hada maza da mata a wajan Maulidi ya kamata a daina yinsa. Saidai Anisee yace a ko inama ana hada maza da mata dan haka su ma a wajan Maulidi ba zasu daina ba.
Faduwar Farashin Abinci: Baku ga komai ba, nan gaba farashin zai kara faduwa sosai kuma gidan kowa sai ya wadata>>Iniji Gwamnatin Tinubu

Faduwar Farashin Abinci: Baku ga komai ba, nan gaba farashin zai kara faduwa sosai kuma gidan kowa sai ya wadata>>Iniji Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya tace 'yan Najeriya basu ga komai ba game da faduwar farashin Abinci da aa gani. Hakan na zuwa ne bayan da hukumar kididdiga ta NBS ta tabbatar da cewa, farashin kayan masarufi yayi ksa a Najeriya inda a yanzu makin bai wuce 20 ba. A yayin hira da manema labarai, me baiwa shugaban kasa shawara akan tattalin arziki, Tope Fasua yace abincin zai sake karyewa sai ya koma kasa da maki 10. Hakan na zuwane yayin da manoma a Arewa ke kokawa da cewa, sune ake hari wannan karya farashin abincin da ake.
Kalli Bidiyo: Akwai wadanda suka fini kudi a Najeriya>>Inji Dangote

Kalli Bidiyo: Akwai wadanda suka fini kudi a Najeriya>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa akwai wanda suka fishi tsabar kudi a Nijeriya. Yace amma basu saka kansu cikin irin rigimar da ya saka kanshi ba. Yana magana ne kan gina matatar man fetur dinsa da kuma rikicin da ya kunno kai tsakaninsa da kungiyar NUPENG. Dangote yace amma dole ne sai an tallafawa gwamnati, yace ba komai ne za'a nade hannu ace wai gwamnati ce zata yi ba. Yace akwai abubuwan da dole sai mutane masu zaman kansu sun saka hannu, yace amma irin abinda ake masa zai sa mutane su guji zuwa zuba hannun jari a Najeriya. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1967987170138079720?t=jK8EwhBa8X1in8Zo76GyHQ&s=19