Friday, December 12
Shadow
Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da Yobe – Nimet

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da Yobe – Nimet

Duk Labarai
Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da Yobe, kamar yadda Hukumar Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar a wani hasashen yanayi da ta fitar a shafinta na X. Hukumar ta ce tsawa da ruwan sama matsakaici na iya sauka a wasu sassan arewacin Najeriya wadda zai iya haddasa ambaliyar ruwan. NiMet ta bayyana cewa da safiyar yau Talata, ana sa ran ruwan sama a jihohin Borno, Yobe, Jigawa, Gombe, Bauchi, Adamawa, Kaduna da Taraba. Hakanan, da yamma zuwa dare, ana sa ran yawancin jihohin Arewa za su ci gaba da samun ruwan sama tare da iska da tsawa. A tsakiyar Najeriya kuwa, hasashen ya nuna cewa za a samu yanayin giragizai da safe, sannan da yamma za a samu ruwan sama matsakaici a wasu sassan Nasarawa, Benue, Kogi, Kwara, Neja, Filato da kuma babban birnin tarayya Abuja. ...
Jihohin Arewacin Najeria ba su nuna aniyar yin rajistar zaɓe sosai ba a makon farko, Jihohin Kudu sun fi nuna Aniya

Jihohin Arewacin Najeria ba su nuna aniyar yin rajistar zaɓe sosai ba a makon farko, Jihohin Kudu sun fi nuna Aniya

Duk Labarai
Bayanan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya - Inec - ta fitar kan alƙaluman makon farko na mutanen da suka nuna aniyar yin rajistar zaɓe ta intanet sun nuna cewa al'umma ba su fito sosai ba a yankin arewacin ƙasar domin yin rajistar. Alƙaluman da hukumar ta Inec ta fitar a jiya Litinin sun nuna cewa jihar Osun ce ta fi yawan mutanen da suka nuna aniyar yin rajistar, inda take da yawan mutane 393,269, jihar Legas ke biye mata da mutum 222,205 sai kuma jihar Ogun mai yawan masu son yin rajista 132,823. A arewacin Najeriya, Abuja, babban birnin tarayyar ƙasar ne ke da mafi yawan mutanen da suka nuna aniyar yin rajista, inda take da mutum 107,683, sai jihar Kaduna mai mutum 61,512 yayin da jihar Kogi ke biye mata da mutum 58,546. ...
Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya sauka daga kan layin dogo

Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya sauka daga kan layin dogo

Duk Labarai
Jirgin ƙasa ɗauke da fasinja da ya taso daga Abuja babban birnin Najeriya zuwa Kaduna ya faɗi a ranar Talata da safe. Lamarin dai ya jefa fargaba a tsakanin fasinjoji da ke cikin jirgin. Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na safe a kauyen Asham da ke hanyar Abuja zuwa Kaduna kuma jirgin ƙasa ta bar Abuja ne da misalin karfe 9:45. Har yanzu ba a san abin da ya jawo saukar jirgin daga kan layin dogo ba, kuma babu tabbacin ko an samu waɗanda suka jikkata. Hukumar Jiragin ƙasar Najeriya (NRC) bata yi tsokaci ba a kan lamarin.
Wata Sabuwa Kalli Bidiyo: Inda wasu ke ikirarin diyar Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) Nana Fadima(AS) ta bayyana a bangon dakin wata mata a garin Zauro na jihar Kebbi

Wata Sabuwa Kalli Bidiyo: Inda wasu ke ikirarin diyar Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) Nana Fadima(AS) ta bayyana a bangon dakin wata mata a garin Zauro na jihar Kebbi

Duk Labarai
Wannan Bidiyon ya watsu sosai inda aka ga wasu mutane a garin Zauro na jihar Kebbi na ikirarin cewa, Diyar Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) Fadima(AS) ta bayyana a bangon dakin wata mata. Mutanen dai sun je inda suke ta tabbatar da ganin Fadima(AS). Sun ce in ma mutum bai yadda ba su dai sun ga abinda suka gani. https://www.tiktok.com/@maiwasida/video/7542184645928996152?_t=ZS-8zC840TOKFF&_r=1 Karin Bidiyo anan: https://www.tiktok.com/@maiwasida/video/7542516711296175416?_t=ZS-8zC9X0II6ds&_r=1
Kalli Bidiyo: Nakwango ya bar harkar fim ya koma yin Wa’azi, Ji abinda yace da mutane ke ta mamakin ashe dan Izala ne?

Kalli Bidiyo: Nakwango ya bar harkar fim ya koma yin Wa’azi, Ji abinda yace da mutane ke ta mamakin ashe dan Izala ne?

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Kabir Nakwango ya bar harkar fim inda ya koma yin wa'azi, An ga Nakwango yana wa'azi shi da majabakinsa. https://www.tiktok.com/@mbbmanaja/video/7542063455717690641?_t=ZS-8zC6ZeboK9J&_r=1 A daya daga cikin Bidiyon wa'azin na Nakwango an ji yana cewa duk abinda bai fito daga bakin Manzon Allah ba, ka barshi. https://www.tiktok.com/@mbbmanaja/video/7542466019961490709?_t=ZS-8zC7Ju5ZQsS&_r=1 Hakan yasa wasu suka fara bayyanashi da cewa ashe dan Ahlussunah ne
Kalli Bidiyo: Tazarar Haihuwa da na yi tasa matata har yanzu da kuruciyarta hakana nima da wuya ka yadda da shekaruna idan na gaya maka, ya kamata kuma ku gwada>>Inji Ali Nuhu

Kalli Bidiyo: Tazarar Haihuwa da na yi tasa matata har yanzu da kuruciyarta hakana nima da wuya ka yadda da shekaruna idan na gaya maka, ya kamata kuma ku gwada>>Inji Ali Nuhu

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Ali Nuhu ya bayyana cewa, yayi tazarar haihuwa kuma haka ya taimaka msa sosai wajan kula da iyalansa da lafiyarsu. Ali Nuhu ya kuma bayyana cewa, hakan yasa har yanzu matarsa na nan da kuruciyarta sannan shima ba lallai a yadda da shekarunsa ba idan ya fada. https://www.tiktok.com/@sadiq_sani_sadiq7/video/7542511809568181510?_t=ZS-8zC5LJbdaSn&_r=1
Duk da kokarin shugaba Tinubu na rage farashin magunguna a Najeriya, Farashin Magungunan sai kara tashi suke

Duk da kokarin shugaba Tinubu na rage farashin magunguna a Najeriya, Farashin Magungunan sai kara tashi suke

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi yunkurin rage farashin magunguna a Najeriya dan samarwa musamman talakawa da masu karamin karfi saukin rayuwa. Saidai duk da wannan, ana ci gaba da samun hauhawar farashin magunguna. A watan Yuni na shekarar 2024 ne Ministan Lafiya,Muhammad Pate ya bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya cire haraji akan magunguna da ake shigowa dasu Najeriya da kayan aikin hada magunguna, musamman dan a saukaka farashin hada magungunan a Najeriya. Saidai rahoton jaridar Punchng yace har yanzu magunguna irin na su hawan jini da zazzabin cizon Sauro da sauransu ba su yi sauki ba.
Bakin da aka ga fuska ta tayi a lokacin da BBChausa suka yi hira dani yawan aski ne yasa amma bana amfani da man kara hasken fata, ni Farine, duka jikina Farina>>Inji Gfresh Al-amin

Bakin da aka ga fuska ta tayi a lokacin da BBChausa suka yi hira dani yawan aski ne yasa amma bana amfani da man kara hasken fata, ni Farine, duka jikina Farina>>Inji Gfresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, duka jikinsa Farine. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo daya wallafa a shafinsa na Tiktok inda yace ko hirar da aka yi dashi a BBChausa aka ga fuskarsa ta yi duhu, saboda yawan aski ne. Gfresh ya kara da cewa, baya amfani da man kara hasken fata. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7542643231998135560?_t=ZS-8zBwLZmWRW4&_r=1
Kalli Bidiyo: Yanda wani yawa  Sheikh Sani Yahya Jingir Ihu a masallaci yace masa nan ba wajan Kamfe bane

Kalli Bidiyo: Yanda wani yawa Sheikh Sani Yahya Jingir Ihu a masallaci yace masa nan ba wajan Kamfe bane

Duk Labarai
Bidiyo ya bayyana inda aka ga wani dalibin babban malamin Izala na Jos, Sheikh Sani Yahya Jingir yana korafi kan wani da yawa malamin Ihun bama so da cewa, nan masallaci ne ba wajan kamfe ba. Dalibin ya bayyana cewa, wannan cin fuska ne ga Malam kuma ba zasu dauka ba, sun sa a nemo musu wadanda sukawa malamin wannan abu. Ya bayyana hakane a shafinsa na Tiktok: https://www.tiktok.com/@saleemyusufmuhammadsambo/video/7542257130359753991?_t=ZS-8zAeQvh2rHU&_r=1
Ji yanda kotu ta daure wata matashiya tsawon shekaru 7 ko ta biya tarar Naira Dubu dari hudu da hamsin bayan da Wani ya aika mata Naira Dubu 150 ta sameshi a gidansa amma ta cinye kudin kuma ta ki zuwa

Ji yanda kotu ta daure wata matashiya tsawon shekaru 7 ko ta biya tarar Naira Dubu dari hudu da hamsin bayan da Wani ya aika mata Naira Dubu 150 ta sameshi a gidansa amma ta cinye kudin kuma ta ki zuwa

Duk Labarai
Wannan matashiyar me suna Jennifer ta fuskanci hukuncin daurin shekaru 7 ko biyan tarar Naira 450 bayan da kotu ta sameta da laifin zamba da bata lokaci. Wani mutum ne me suna Emmanuel ne da suka hadu a kafar sada sumunta ya aika mata da Naira dubu 150 dan ta sameshi a Abuja. Saidai ta cinye kudin kuma ta ki zuwa ta biya masa bukata. Dalilin hakane ya kaita kotu. Kotu dai ta sameta da laifin zamba da bata lokaci dan haka aka yanke mata hukuncin Daurin shekaru 7 a gidan yari ko biyan tarar Naira dubu. 450