Wani Dansandan Najeriya ya sha giya yayi Mankas yana marisa inda aka dauki Bidiyonsa yana tambele.
Da yawa dai sun bayyana rashin jin dadinsu da faruwar hakan
https://www.tiktok.com/@africafunny1/video/7570671122342038796?_t=ZS-91HgtZboNIv&_r=1
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, zai Rabawa mutanen kasarsa dala $2000 kowanne daga kudin Harajin da ya tara daga hannun kasashen Duniya.
Ya bayyana hakane a shafinsa na Truth social inda yace kasarsa ce kasa da aka fi girmamawa a tsakanin kasashen Duniya
Sannan ya yi alkawarin yin amfani da kudin Harajin wajan biyan bashin da ake bin kasar Amurka.
Saidai da yawa 'yan kasar ta Amurka na shakka akan wannan ikirari nasa.
Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu ya bayyana cewa Allah ya riga ya kaddarowa Atiku Abubakar cewa ba zai zama shugaban kasar Najeriya ba.
Yayi kira ga Atiku da ya hakura da kaddarar da Allah ya doro masa cewa ba zai zama shugaban Najeriya.
Atiku dai tin a shekarar 1992 yake neman takarar shugabancin Najeriya amma bai samu ba.
Ya bayyana hakane ga manema labarai a fadarsa yayin da yake bikin cika shekaru 22 da hawa karagar sarautar Birnin na Legas.
Yace shi kuma Tinubu zabin Allah ne dan haka yana kira ga 'yan Najeriya da su goya masa baya.
Tauraron Mawaki Soja Boy ya sake sakin wata sabuwar wakarsa inda suka yi shi dame shafin Home of Luxury.
An gansu a Bidiyon da Soja Boy ya wallafa suna wakar tare inda daga baya ta rungumeshi.
https://www.tiktok.com/@officialsojaboyy/video/7570847225937513748?_t=ZS-91HPVPRHLcn&_r=1
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin Tarayya ta ciwo bashi fiye da yanda ta yi niyyar ciyowa a shekarar 2025.
A kasafin kudin shekarar 2025, Gwamnati ta yi niyyar ciwo bashin Naira Tiriliyan 13.08 saidai zuwa yanzu har ta ciwo bashin Naira Tiriliyan 17.36.
Hakan na nufin Gwamnatin ta ciwo bashin Naira Tiriliyan N6.06 sama da abinda ta yi niyyar ciyowa a wannan shekarar tun ma shekarar bata kare ba.
Gwamnatin taci bashin naira Tiriliyan N15.8 daga cikin gida Najeriya sai kuma bashin Naira Tiriliyan 1.56 daga kasashen waje.
A satin daya gabata ne dai Gwamnatin ta bayyana aniyar son ciwo bashin Naira Tiriliyan N3.384 daga kasashen Turai.
Dan majalisar wakilai ta tarayya, Abdulmumin Jibrin Kofa dake wakiltar mazabun Kiru/Bebeji ya bar jam'iyyar NNPP ya kpma jam'iyyar APC.
Ya bayyana hakan ne ranar Litinin a sakon da ya fitar a shafinsa na sada zumunta.
Hakan na zuwane watanni 2 bayan da jam'iyyar NNPP ta koreshi bisa zargin yana mata zagon kasa da kuma kin biyan kudaden harajin jam'iyyar.
Komawarsa APC bata zowa mutane da bazata ba musamman lura da yanda yake da alaka me kyau da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Ya bayyana cewa yana goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027 sannan kuma yace malamai 2000 ne sukawa shugaba Tinubu da Najeriya addu'a a mazabarsa.
Jam'iyyar APC ta fara yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kin neman zaben shekarar 2027
Matar shugaban jam'iyyar APC, Dr Martina Yilwatda ce ta fara wannan yakin neman zaben a Abuja.
Ta halarci wani taro na mata 'yan jam'iyyar APC ne da aka shirya inda tace lokaci yayi da zasu fara yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yakin neman zabe inda ta yi kira ga matan da su rika jawo hankulan 'yan uwansu mata wajan sakw zaben shugaba Tinubu.
Tace Tinubu yawa Najeriya da mata abubuwan ci gaba sosai dan haka ya cancanci a sake zabensa a karo na 2.
An yi sa insa tsakanin Majalisar Koli ta Addinin Musulunci NSCIA da kungiyar Kiristoci ta PFN a Najeriya.
Inda majalisar koli ta Addinin Musulunci a Najeriya take cewa babu maganar Khisan kiyashi da akewa mutane a Najeriya.
Ta zargi wasu bata gari a Najeriya bisa hadin gwiwar wasu 'yan kasashen yamma da shirin amfani da sunan ana Mhuzghunawa Kiristoci su lalata Najeriya.
Sakataren kungiyar NSCIA, Prof. Is-haq Oloyede a yayin da yake ganawa da manema labarai a Abuja ranar Lahadi ne ya bayyana hakan.
Yace rikicin Najeriya ba na addini bane, Canjin yanayi, da Talauci, da Aikata Miyagun Laifuka, da rashin shugabanci na garine ya jawo abinda ke faruwa a Najeriya.
Saidai a nasa bangaren, shugaban kungiyar Kiristoci ta PFN,Bishop Wale Oke ya bayyana cewa, maganar gaskiya anawa K...
Rahotanni sun bayyana cewa, Najeriya ta tafka Asarar Naira Biliyan N824.66bn a shekarar 2024 a kasuwancin Danyen Man fetur.
Hakan ya bayyana ne a cikin rahotannin da ofishin kasafin kudi na tarayya ya fitar.
A shekarar 2023 gwamnatin tarayyar ta samu kudin shiga da suka kai Naira Tiriliyan N1.90tn saidai a shekarar 2024 kuma ta samu Naira Tiriliyan N1.08tn ne wanda hakan ke nuna an samu raguwar kaso 43.32 cikin 100 na kudin shigar daga kasuwancin Danyen man fetur.
Wannan bayanai na watanni 3 ne na karshen shekara bana gaba dayan shekarar ba.
Wasu matasa, Namiji da Mace sun bayyana a Shafin Tiktok sun bayyana suna aikata bhadala da ba'a taba yin irinshi a Arewa ba.
An gansu suna Runghume-Rhungume suna Sumbatar Juna da shiga daki da niyyar aikata Jima'i
Daa yawan mutane dai sun fito suna ta Allah wadai dasu.
https://www.tiktok.com/@aisha.usman512/video/7569861355868589319?_t=ZS-91GBVYfQ29R&_r=1