Rahotanni sun ce 2 daga cikin sojojin da ake zargi da yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Jhuyin mulki sun tsere.
Jaridar Cable ce ta ruwaito labarin inda tace cikinsu akwai JM Ganaks wanda ke da mukamin Major da lambar aiki N/14363 sannan yana aiki ne a Jaji.
Sannan akwai G Binuga wanda shi kuma Captai ne me lambar aiki N/167722 wanda dan Asalin jihar Taraba ne.
Thecable tace zuwa yanzu akwai sojoji 30 da ake tsare dasu ake tuhumarsu bisa zargin yunkurin yin Jhuyin mulkin.
A yau ne hukumar sojojin Najeriya zata yi bikin kammala aikin tsohon shugaban sojojin Najeriya, CG Musa.
A yau za'a yi bikin dan tunawa da irin gudummawar da ya kawowa gidan soja da nasarorin da ya samu da sauransu.
Sanarwar data fito ranar Alhamis tace za'a gudanar da fareti dan hakan.
An fitar da jadawalin kasashen da mutane suka fi shan wahalar rayuwa a Duniya kuma Najeriya ce ta zo ta daya.
Ga Jadawalin kasashen kamar haka:
Nigeria
Bangladesh
Venezuela
Sri Lanka
Egypt
Iran
Peru
Vietnam
Philippines
Lebanon
Kenya
Indonesia
Pakistan
Albania
Thailand
Rahotanni sun ce hukumar sojojin Najeriya ta canjawa manyan sojoji 60 guraren aiki.
Hakan na kunshe a wata sanarwa ne data bayyana a yau 30 ga watan October inda aka ce sojojin su koma sabbin guraren aikin da aka turasu nan da 3 ga watan Nuwamba.
Tun ranar Juma'ar data gabata ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince da canjawa manyan sojojin wajan aiki.
Hakan na zuwane bayan bayyanar rahotanni dake cewa an yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu juyin mulki.
A dazu ne muka kawo muku Rahoton sunayen sojoji 16 wadanda ake zargin sun shiryawa shugaba Tinubu juyin mulki aka kuka kamasu.
A yanzu fuskokin wasu daga cikin sojojin sun fara bayyana.
Daga ciki akwai M.A Sadiq da kuma MA Ma'aji.
Rahotanni dai sun ce an kama karin sojoji 26 bisa zarginsu da hannu a lamarin.
Rahotanni sun ce a cikin sojojin da aka kama da zargin yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki, SB Adamu ne aka baiwa aikin Shekye babban me baiwa shugaban kasa, shawara kan tsaro, watau Malam Nuhu Ribadu.
Shi dai SB Adamu an kaishi aiki ofishin Malam Nuhu Ribadu wanda kuma aka bashi aikin ya kula dashi ya shekye.
Kafar Thecable ce ta ruwaito labarin inda tace wata majiyar gidan soji ce ta sanar da ita hakan.
Tace ba kamar yanda ake yadawa cewa sauran sojojin da suka shirya juyin mulkin a ofishin me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro suke ba, tace SB Adamu ne kadai a ofishin.
Majiyar sojin tace wannan alamace dake nuna cewa masu juyin mulkin sun kama manyan sojoji sosai a gidan sojan.
Rahotanni daga majalisar dattijai na cewa akwai alamu masu karfi dake nuni da cewa, an shirya tsakanin Sanata Natasha Akpoti da Sanata Godswill Akpabio.
Hakan ya bayyana ne bayan da sanata Natasha Akpoti ta gayyaci Sanata Godswill Akpabio zuwa mazabarta Ihima, Kogi da kaddamar da wani aiki da ta yi.
Sanata Godswill Akpabio ne ya karanta takardar gayyatar a zauren majalisar Dattijai ranar Alhamis inda tace tana gayyatarshi da sauran sanatocin zuwa kaddamar da aikin.
A baya dai Sanata Natasha Akpoti ta zargi Sanata Godswill Akpabio ta neman ta da lalata wanda lamarin ya jawo zazzafar Muhawara.
Babban yaron Nazir Ahmad Sarkin Waka, Abba C Sale yace ya janye maganar da ya taba yi a baya wadda ta jawo cece-kuce sosai a kafafen sada zumunta.
Abba ya taba cewa, yana samun Naira Miliyan 5 a wata wanda hakan yasa mutane sukaita cece-kuce inda wasu da dama suka rika karyatashi.
Idan ya wallafa Bidiyo akan rika rubuta masa 5M a comment kuma ya sha yin gargadin cewa baya so amma da yawa basu daina ba.
A yanzu dai yace ya janye waccan magana kuma kada a sakw masa maganar idan ba haka ba zai dauki mataki.
https://www.tiktok.com/@abbacsale2/video/7567051318188133653?_t=ZS-90zDPeqx1Bh&_r=1
Wata sabuwar waka da Naziru Sarkin Waka yayi i da aka ga 'yan Rawarsa sanye da kayan 'yansanda ta jawo cece-kuce.
Wasu dai na ganin cewa hakan rashin ganin girman 'yansanda ne inda wasu kuma ke cewa ba komai bane.
Danna nan dan kallon Bidiyon wakar
https://www.tiktok.com/@sadeeqking__/video/7566789692826438924?_t=ZS-90zBtby2q3t&_r=1