Thursday, February 26
Shadow
An baiwa Babban Bankin Najeriya, CBN shawarar fito da takardun kudi na Naira 20,000 da 10,000

An baiwa Babban Bankin Najeriya, CBN shawarar fito da takardun kudi na Naira 20,000 da 10,000

Duk Labarai
Wata kungiya me suna Quartus Economics ta bada shawara ga babban bankin Najeriya da ya fito da takardar kudin Naira 20,000 da 10,000. Kungiyar tace dalili kuwa shine a yanzu takarar Naira 1000 bata iya sayen wani abin a zo a gani. Tace fito da manyan kudaden zai ragewa mutane wahalar daukar kudade da yawa wajan gudanar da kasuwanci. Ungiyar tace ba gaskiya bane abinda ake fada cewa idan aka fito da sabbin kudin zasu iya saka farashin kayan masarufi su tashi. Kungiyar tace darajar Naira ta lalace sosai.
Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saka harajin kaso 15 kan Man fetur da Gas

Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saka harajin kaso 15 kan Man fetur da Gas

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban kasa na cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince ko ya saka hannu kan kudirin dokar saka Harajin kaso 15 cikin 100 akan man fetur da gas da ake shigowa dasu Najeriya. Sakataren shugaban kasar, Damilotun Aderemi ne ya dauki takardar kudirin dokar inda ya kaiwa hukumomin da lamarin ya shafa dan a fara zartas da wannan doka. Ana tsammanin wannan sabuwar dokar haraji zata kara farashin man fetur da akalla N0.99, kamar yanda The Cable ta ruwaito.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayar da Umarnin a dawo a ci gaba da yin Gwajin Makamin kare dangi

Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayar da Umarnin a dawo a ci gaba da yin Gwajin Makamin kare dangi

Duk Labarai
Republican presidential candidate and former U.S. President Donald Trump looks on in the courtroom, as his criminal trial over charges that he falsified business records to conceal money paid to silence porn star Stormy Daniels in 2016 continues, at Manhattan state court in New York City, U.S., April 23, 2024. REUTERS/Brendan Mcdermid/Pool Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya baiwa ma'aikatar yaki ta kasarsa umarnin a dawo a ci gaba da gwajin makamin kare dangi, watau Nokiliya. Shugaban yace idan dai wasu kasashe zasu rika yin gwajin bai ga dalilin da zai hana kasar Amurka itama ta rika yin irin wannan gwajin ba. Saidai masu sharhi sun ce abinda suka fahimta shine shugaban ba yana nufin a rika harba makamin bane, yana nufin a rika gwadawa Duniya Kwajin kasar Amurka ne. Hakan...
Kasar Saudiyya zata gina Filin Kwallon kafa(Stadium) wadda babu irinta a Duniya

Kasar Saudiyya zata gina Filin Kwallon kafa(Stadium) wadda babu irinta a Duniya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kasar Saudiyya ta sanar da shirinta na gina filin Kwallon kafa( Stadium) wanda babu irinsa a Duniya. Filin za'a ginashi ne a sararin samaniya wanda masana suka ce zai yi nisan kafa 1,150 daga kasa. Sannan zai dauki mutane 46,000. Sannan za'a ginashine a shekarar 2032. Wannan na daga cikin kokarin kasar ta Saudiyya na samun daukar nauyin wasan cin kofin kwallin Duniya na shekarar 2034. Hakanan gina Filin zai ci kudi har dala Biliyan $1.
Rikyichin Bana da A’isha Humaira ya dauki sabon salo, Ya saki Bidiyon bada Hakuri saidai ya sake sakin Wani Bidiyo yana cewa an tura masa wasu hatsabibai

Rikyichin Bana da A’isha Humaira ya dauki sabon salo, Ya saki Bidiyon bada Hakuri saidai ya sake sakin Wani Bidiyo yana cewa an tura masa wasu hatsabibai

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa kuma dan Tiktok Bana ya fito ya baiwa masoyansa da 'yan uwa hakuri bayan Bidiyon da ya saki yana sukar A'isha Humaira da mijinta Rarara. https://www.tiktok.com/@danmutum.1/video/7566715571908136212?_t=ZS-90xvC6UMcMb&_r=1 Saidai jim kadan bayan sakin Bidiyon sai ga Bana ya sake sakin wani Bidiyon yana cewa, ya koma gida ya iske an aika masa wasu tsagera. Yace dai ko me ya sameshi su za'a kama. https://www.tiktok.com/@danmutum.1/video/7566768327004065044?_t=ZS-90xwaZM4LJp&_r=1 Tun Farko dai Bana ya wallafa Bidiyon inda ya soki Rarara game da wani Bidiyo da yayi zargin cewa Rarara din ya kama kugun wata Amarya. Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai inda har sai da A'isha Humaira ta ce masa ya goge Bidiyon sannan ya bada hakuri nan da sati ...
Majalisar Dattijai na tantance manyan hafsoshin sojin Najeriya

Majalisar Dattijai na tantance manyan hafsoshin sojin Najeriya

Duk Labarai
Majalisar dattijan Najeriya na aikin tantance manyan hafsoshin sojin ƙasar waɗanda shugaban ƙasar Bola Tinubu ya zaɓo domin jan ragamar ɓangaren tsaro na ƙasar. Manyan hafsohin sojin sun isa harabar majalisar da misalin ƙarfe 10 zuwa 11 na safe. Da farko majalisar ta bayyana cewa za ta gudanar da tantancewar ne a mako mai zuwa, sai dai daga baya ta yanke shawarar matso da tantancewar zuwa yau Laraba Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya, a ranar Talata, ya ce akwai buƙatar gaggauta tantance shugabannin tsaron domin ba su damar ci gaba da gudanar da ayyukansu. A ranar 24 ga watan Oktoba ne Shugaba Tinubu ya gudanar da sauye-sauye a jagorancin ɓangaren tsaro na ƙasar, inda aka sauya hafsan hafson ƙasar Christopher Musa da Laftanar-Janar Olufemi Olatubosun Oluyede. Haka nan shug...
Kalli Hotunan ‘Yar Takarar Gwamna a jihar Anambra karkashin Tutar jam’iyyar AAC data jawo cece-kuce sosai

Kalli Hotunan ‘Yar Takarar Gwamna a jihar Anambra karkashin Tutar jam’iyyar AAC data jawo cece-kuce sosai

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Chioma Ifemeludike ta bayyana aniyarta ta takarar gwamnan jihar Anambra karkashin jam'iyyar AAC. Tace itace da nasara a wannan zabe. Saidai hotunan yakin neman zaben nata sun jawo cece-kuce inda wasu ke cewa basu dace ba wasu kuma na cewa ba yakin neman zabe ta fito ba wani abu dai take son cimmawa.
Ji yanda aka kama matashi da zargin aikata Alfasha da matar abokin mahaifinsa

Ji yanda aka kama matashi da zargin aikata Alfasha da matar abokin mahaifinsa

Duk Labarai
An kama wasu 'yansanda 3 saboda dukan wani matashi me suna Jacob Sunday dan kimanin shekaru 22. Aun zargeshi ne da yin lalata da matar abokinsu a barikin 'yansanda dake 22 PMF Barracks, Ogudu a jihar Legas. Lamarin ya farune ranar Talata da misalin karfe 6 na yamma. 'Yansandan da aka kama sune Inspector John Alom, Inspector Sunday Adoga, da kuma Inspector Jehovah Usam wadanda duka a barikin suke zaune. Mahaifin matashin sunansa  Inspector Sunday Ochepo kuma an zargeshi ne da yin lalata da matar ASP Audu Richard me suna Sarah Richard Sun yiwa yaron tsirara suka rika dukansa har sai da ya suma, an garzaya dashi zuwa Asibiti inda su kuma aka kamasu.
Mutane 2 sun rigamu gidan gaskiya wasu da dama suka Jhikkata sanadiyyar Rikyichin Limancin masallacin Juma’a a jihar Taraba

Mutane 2 sun rigamu gidan gaskiya wasu da dama suka Jhikkata sanadiyyar Rikyichin Limancin masallacin Juma’a a jihar Taraba

Duk Labarai
Mutane 2 ne suka rasu wasu da dama suka samu raunuka sanadiyyar fadan da ya barke tsakanin musulmai a saboda tababar wanene zai yi limancin masallacin Juma'a na garin Donga dake jihar Taraba. Daily Trust ta ruwaito cewa bayan asarar rayuka da jikkata wasu an kuma tafka asarar dukiya Saidai Tuni an kai jami'an tsaro garin kamar yanda rahoton ya nunar. An yi kokarin jin ta bakin kakakin 'yansandan jihar, ASP Leshen James amma abu yaci tura.