Friday, February 27
Shadow
Sabon Rahoton ya yi bayani dalla-dalla yanda wasu sojoji suka so yiwa shugaba Tinubu juyin mulki, Sun so su aika shugaba Tinubu, Kashim Shettima, Akpabio da Tajudeen Abbas Qhiyama

Sabon Rahoton ya yi bayani dalla-dalla yanda wasu sojoji suka so yiwa shugaba Tinubu juyin mulki, Sun so su aika shugaba Tinubu, Kashim Shettima, Akpabio da Tajudeen Abbas Qhiyama

Duk Labarai
A baya mun samu rahoto daga Sahara reporters cewa an kama wasu sojoji 16 da suka yi yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki. Duk da hukumar sojoji tace sojojin sun aikata wasu laifuka ne na rashin da'a, Saidai Sahara reporters tace juyin Mulki ne sojojin suka shirya amma ake boye maganar. Hakanan kafar Premium times itama ta tabbatar da cewa aojojin sun shiryawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin mulki ne. Hakanan an kamasu ne tun kamin ranar 1 ga watan October, sannan su kusan 20 ne a cewar Sahara reporters Hakanan premium times tace sojojin sun shirya yin juyin mulkinne ranar 25 ga watan October inda suka so kashe ahugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima da kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio, dana wakilai, Tajudeen Ab...
Allah Sarki: Ji Yanda matar aure ta yanke jiki ta fadi sumammiya bayan da mijin ta ya saketa a Kotu, Ta kai karane inda tace Alkali ya hana mijin sakinta saboda bata so su ramu amma mijin yace shi baya sonta

Allah Sarki: Ji Yanda matar aure ta yanke jiki ta fadi sumammiya bayan da mijin ta ya saketa a Kotu, Ta kai karane inda tace Alkali ya hana mijin sakinta saboda bata so su ramu amma mijin yace shi baya sonta

Duk Labarai
Wata matar aure Mulikat Yusuf ta yanke jiki ta fadi sumammiya bayan da mijinata ya saketa a kotu duk da kai kara da ta yi akan kada ya saketa. Matar ta kai mijinta, Ishaq Abdulganiyu kara inda tacewa kotu ta haifa masa yara 6 kuma ita yanzu idan ya saketa bata san inda zata ba. Saidai mijin yace babu ruwansa da ita. A hanyarta ta fita daga kotun ta yanke jiki ta fadi. Saida aka yayyafa mata ruwa ta farfado. Lamarin ya farune a kotun dake Igboro, Ilorin jihar Kwara. Alkalin kotun, Toyin Oluko ya baiwa matar shawara ta je ta lallaba mijinta. An daga ci gaba da sauraren shari'ar har zuwa 5 ga watan Disamba, inda alkalin yace ya basu damar su shirya kamin lokacin ko kuma a ci gaba da shari'a.
Hukumar Sojojin Najeriya ta yi martani kan rahoton juyin Mulki

Hukumar Sojojin Najeriya ta yi martani kan rahoton juyin Mulki

Duk Labarai
Hedikwatar Tsaron Nijeriya Ta Karyata Zargin Yunƙurin Juyin Mulki A wani jawabi da ta fitar don fayyace dalilin soke bukukuwan samun 'Yancin Kai, Hedikwatar Tsaron Najeriya ta musanta jita-jitar da ke yawo kan zargin yunƙurin juyin mulki. A cikin wata sanarwa da Birgediya Janar Tukur Gusau ya rattaba wa hannu, hedikwatar ta ce an soke bikin samin ƴancin kan ne don bai wa sojojin Najeriya damar mayar da hankali kan yaƙi da suke da ta'addanci da ƴan bindiga, kana da bai wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu sararin halartar wani taro mai muhimmanci kan kyautata dangantakar kasa da kasa. Rundunar ta kuma yi ƙarin haske kan binciken da ake ci gaba da yi kan zargin wasu jami'anta 16 da nuna rashin ɗa'a wajen aiki, inda ta tabbatar wa 'yan Najeriya cewa zargin ya dogara ne kan aiyukan soji na ya...
Kalli Bidiyo: Shekaruna 29 amma har yanzu ban yi aure ba, har kudi na kashewa Samari amma har yanzu ba wanda ya fito da niyyar aurena, ina zan saka kaina? Matashiya ta fashe da kuka

Kalli Bidiyo: Shekaruna 29 amma har yanzu ban yi aure ba, har kudi na kashewa Samari amma har yanzu ba wanda ya fito da niyyar aurena, ina zan saka kaina? Matashiya ta fashe da kuka

Duk Labarai
Wannan matashiyar 'yar Najeriya ta fashe da kuka a wani Bidiyo data wallafa inda tace kadan ya rage ta kai shekaru 29 amma har yanzu bata da mijin aure. Ta bayyana hakane a wani Bidiyo ta da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda tace laifin me ta aikata, tace tana da hali me kyau, har kudi take kashewa samari amma har yanzu bata samu mijin aure ba. Wannan Bidiyon nata ya jawo zazzafar Muhawara a kafafen sadarwa. https://twitter.com/dammiedammie35/status/1979443581778825327?t=E8JUTsHz_dy0PccfA-2P8w&s=19
Ashe Maganar Juyin Mulki Gaskiya ce, shiyasa naga manyan kasar Hadda Tinubu sun tafi kasashen waje ta yanda idan an yi juyin Mulkin zasu samu sauki>>Inji Tsohuwar Hadimar Shugaban kasa, Lauretta Onochie

Ashe Maganar Juyin Mulki Gaskiya ce, shiyasa naga manyan kasar Hadda Tinubu sun tafi kasashen waje ta yanda idan an yi juyin Mulkin zasu samu sauki>>Inji Tsohuwar Hadimar Shugaban kasa, Lauretta Onochie

Duk Labarai
Tsohuwar hadimar shugaban kasa a zamanin Mulkin shugaba Muhammadu Buhari, Lauretta Onochie ta bayyana cewa ashe maganar juyin mulkin gaskiyace. Tace shiyasa suka ga manyan kasar hadda shugaban kasa sun tafi kasashen waje ta yanda idan an yi juyin mulkin zasu samu sauki. Ta bayyana hakane a shafinta na X. https://twitter.com/Laurestar/status/1979487065558413410?t=LnL_Po2oag7OFwu1jF5xxQ&s=19 Hakan na zuwane bayan da Sahara reporters ta ruwaito cewa, an kama wasu janarorin soji 16 da suka yi yunkurin yiwa Gwamnatin Tinubu juyin mulki.
Tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello da EFCC ke bincike kan zargin Satar Naira Biliyan 80 yace shugaba Tinubu ba sai ya je jikar Kogi yakin neman zabe ba, ya ci zaben 2027 a jihar

Tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello da EFCC ke bincike kan zargin Satar Naira Biliyan 80 yace shugaba Tinubu ba sai ya je jikar Kogi yakin neman zabe ba, ya ci zaben 2027 a jihar

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu tabbaci cewa, ba sai ya je yakin neman zabe ba jihar Kogi. Yace shugaban ne zai yi nasara a zaben shekarar 2027 me zuwa. Ya bayyana hakane a wajan yakin neman zabe inda ake nuna goyon bayan ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da kuma gwamna Usman Ododo na jihar kan su zarce a karo na biyu.
Dan Shugaban kasa, Seyi Tinubu ya baiwa ‘yar Fim Kyautar Naira Miliyan 20

Dan Shugaban kasa, Seyi Tinubu ya baiwa ‘yar Fim Kyautar Naira Miliyan 20

Duk Labarai
Dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ya baiwa 'yar Fim, Sarah Martins kyautar Naira Miliyan 20. Sarah Martins dai ta gamu da fushin hukumomi a Legas inda suka hukuntata bayan da ta dafawa marasa karfi Abinci akan titin Legas. Saidai Dan shugaban kasar ya share mata hawaye ta hanyar bata kyautar Naira Miliyan 20. Lamarin ya dauki hankula sosai inda ake ta cece-kuce da zazzafar Muhawara
Emmanuel Efayeta Kuejubola ya aikawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu budaddiyar wasika inda yake neman ya bashi bashin Naira 12 zai yi kasuwanci

Emmanuel Efayeta Kuejubola ya aikawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu budaddiyar wasika inda yake neman ya bashi bashin Naira 12 zai yi kasuwanci

Duk Labarai
Wani mutum dan jihar Delta me suna Emmanuel Efayeta Kuejubola ya aikawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da budaddiyar wasika inda yake neman shugaban kasar ya bashi bashin Naira Biliyan 12. Yace burinsa shine ya gina gidaje 400 masu dakina 2 a jiharsa ta Delta. Yace idan aka bashi bashin, nan da watanni 36 zai mayar da kudin ya biya bashin. Yace a baya ya taba aikawa Dangote irin wannan wasika amma bai sami amsa ba. Yace yana fatan a wannan karin zai samu amsa daga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Kalli Bidiyon: Idan kuka ganni Ina Saka Hotuna ko Bidiyon Tsyraychi ko kuka ga ina Aikata Alfasha da wani kada wanda ya sake min gargadi ko yace inji tsoron Allah saboda na dade ina rokon a Taimakeni dan Allah babu wanda ya kulani, dan haka zan ci gaba da bada jikina>>Inji Maryam Buzuwa

Kalli Bidiyon: Idan kuka ganni Ina Saka Hotuna ko Bidiyon Tsyraychi ko kuka ga ina Aikata Alfasha da wani kada wanda ya sake min gargadi ko yace inji tsoron Allah saboda na dade ina rokon a Taimakeni dan Allah babu wanda ya kulani, dan haka zan ci gaba da bada jikina>>Inji Maryam Buzuwa

Duk Labarai
'Yar Tiktok Maryam Buzuwa ta dauki hankula sosai bayan da ta wallafa wani Bidiyo tana cewa zata ci gaba da nuna tsitaici da kuma bayar da jikinta tana samun abinda take so. Tace dalili shine ta nemi a bata dan Allahu babu wanda ya kulata. Sannan tace kada wanda ya sake ce mata ta daina ko ta ji tsoron Allah. Tace ko Iftihal Madaki bata ga laifinta ba itama kwanannan za'a ganta tare da su Soja Boy din. https://www.tiktok.com/@maryambuzuwa20/video/7552927061925645576?_t=ZS-90eUwmASTDt&_r=1
Da Duminsa: Wasu sojojin Najeriya sun Shirya yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki saidai an yi nasarar kamasu kamin su ida nufinsu

Da Duminsa: Wasu sojojin Najeriya sun Shirya yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki saidai an yi nasarar kamasu kamin su ida nufinsu

Duk Labarai
Rahotanni daga kafar Sahara reporters wanda tace ta samo ta wasu majiyoyi sun ce wasu sojoji sun yi yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki. Sojojin sun shirya juyin Mulkinne ranar 1 ga watan Oktoba ta hanyar harbe shugaban kasar da wasu manyan jami'an tsaronsa sannan su ayyana gwamnatin Soja. Rahoton yace sojoji 16 yanzu haka suna hannu wadanda suka fara daga mukamin Kaftin zuwa Brigadier General bisa wannan zargi. Sahara reporters tace hukumar sojin tace an kama sojojin ne bisa laifuka daban-daban da suka aikata amma ba haka bane gaskiyar lamarin. Majiyar tace an ce sun aikata wasu laifukane kawai dan ba'a so maganar ta fita.