Sabon Rahoton ya yi bayani dalla-dalla yanda wasu sojoji suka so yiwa shugaba Tinubu juyin mulki, Sun so su aika shugaba Tinubu, Kashim Shettima, Akpabio da Tajudeen Abbas Qhiyama
A baya mun samu rahoto daga Sahara reporters cewa an kama wasu sojoji 16 da suka yi yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki.
Duk da hukumar sojoji tace sojojin sun aikata wasu laifuka ne na rashin da'a, Saidai Sahara reporters tace juyin Mulki ne sojojin suka shirya amma ake boye maganar.
Hakanan kafar Premium times itama ta tabbatar da cewa aojojin sun shiryawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin mulki ne.
Hakanan an kamasu ne tun kamin ranar 1 ga watan October, sannan su kusan 20 ne a cewar Sahara reporters
Hakanan premium times tace sojojin sun shirya yin juyin mulkinne ranar 25 ga watan October inda suka so kashe ahugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima da kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio, dana wakilai, Tajudeen Ab...








