Wednesday, July 9
Shadow
Kuma Dai:Farashin danyen man fetur da Najeriya ke fitarwa zuwa kasar waje ya tashi inda hakan ke barazana ga kudin shigar Gwamnatin Tinubu

Kuma Dai:Farashin danyen man fetur da Najeriya ke fitarwa zuwa kasar waje ya tashi inda hakan ke barazana ga kudin shigar Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, farashin danyen man fetur da Najeriya ke fitarwa zuwa kasashen waje da ake kira da Brent crude oil ya sake faduwa. Farashin a yanzu ya doso Dala $70 akan kowace ganga. Hakan dai ya farune ranar Laraba inda aka alakanta dalilin da cewa Rasha ce dake shirin fara kara yawan man fetur din da take fitarwa zuwa kasuwar Duniya. Hakanan Suma kungiyar Kasashe masu arzikin Man fetur, OPEC suna shirin kara yawan man fetur din da suke fitarwa wanda hakan zai iya kara karya farashin. Kasancewar Najeriya a matsayin kasa wadda mafi yawan kudaden shigarta daga sayar da danyen man fetur suke zuwa yasa karayar farashin kewa kudaden shigar gwamnatin kasar barazana.
Ji abinda sojoji sukawa Gwamna Fubara bayan dakatar dashi da Shugaba Tinubu yayi wanda mutane da yawa ke cewa cin zali ne

Ji abinda sojoji sukawa Gwamna Fubara bayan dakatar dashi da Shugaba Tinubu yayi wanda mutane da yawa ke cewa cin zali ne

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Rivers sun ce bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da Gwamna Simi Fubara da mataimakinsa da Majalisar jihar, Ya baiwa sojoji umarnin kula da jihar. Tuni dai rahotanni suka bayyana cewa sojojin sun kai motocinsu da tankokin yaki gidan gwamnatin jihar. Sojojin kamar yanda rahoton jaridar Peoplesgazette ya nunar sun tsare Gwamna Fubara a gidan gwamnatin jihar ta Rivers shi da iyalinsa inda suka hanasu zuwa ko ina. Rahoton yace jim kadan bayan da Shugaba Tinubu ya dakatar da gwamna Fubara, sai sojojin suka kulle duka kofofin shiga da fita na gidan gwamnatin jihar. Rahoton yace Gwamna Fubara da iyalansa sun yi kokarin tattara kayansu dan ficewa daga gidan gwamnatin amma aka hanasu saboda sojojin sun hana shiga da fita daga cikin gidan gwamnatin j...
APC ta goyi bayan Shugaba Tinubu kan saka dokar ta baci a jihar Rivers inda ta gargadi wani Gwamna tace yayi hankali saura shi

APC ta goyi bayan Shugaba Tinubu kan saka dokar ta baci a jihar Rivers inda ta gargadi wani Gwamna tace yayi hankali saura shi

Duk Labarai
Sakataren jam'iyyar APC, Ajibola Basiru ya bayyana goyon bayan jam'iyyar su ga matakin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauka na dakatar da gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara. A sanarwar da ya fitar daga kasar Saudiyya, Basiru yace lamuran tsaro sun runcabe a jihar Rivers amma gwamnan jihar ya ki tashi tsaye ya dauki mataki. Yace suna fatan wannan mataki da shugaban kasa ya dauka ya kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar. Ya kara da kira ga shugaba Tinubu da ya dauki irin wannan mataki akan jihar Osun inda ya zargi gwamnan jihar da dakile ayyukan kananan hukumomi duk da umarnin kotu.
Gwamnonin PDP sun nemi shugaba Tinubu ya mayar da Fubara a matsayin gwamnan jihar Rivers inda sukace zasu kai shugaban kasar Kotu

Gwamnonin PDP sun nemi shugaba Tinubu ya mayar da Fubara a matsayin gwamnan jihar Rivers inda sukace zasu kai shugaban kasar Kotu

Duk Labarai
Kungiyar gwamnonin PDP sun sha Alwashin kai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kara a kotu saboda dakatar da gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara inda ya kakaba dokar ta baci a jihar. A sanarwar da suka fitar ta bakin Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, PDP sun ce shugaba Tinubu ya amince yayi kuskure sannan ya mayar da Fubara kan kujerarsa ta gwamna. Gwamnonin na PDP sun zargi shugaban kasar da nuna bangaranci wajan daukar wannan mataki inda suka ce yaki ya bayyana kuskuren Ministan Abuja, Nyesome Wike wajan jefa jihar ta Rivers a halin data tsinci kanta. Kungiyar gwamnonin tace tana tare da mutanen jihar Rivers a wannan tsaka mai wuya da suka tsinci kansu, sannan sunce auna tare da kungiyar Lauyoyin Najeriya, NBA da tace wannan mataki ya sabawa doka. Kungiyar Gwamnonin tace...
Rikicin jihar Rivers baikai matsayin da za’a ce a saka dokar ta baci ba>>Inji Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya, NBA

Rikicin jihar Rivers baikai matsayin da za’a ce a saka dokar ta baci ba>>Inji Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya, NBA

Duk Labarai
Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya, NBA ta bayyana cewa, Rikicin jihar Rivers bai kai matakin da za'a ce a saka dokar ta baci ba. Kungiyar a sanarwar data fitar bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya saka dokar ta baci a jihar Rivers tace tabbas kundin tsarin mulki ya baiwa shugaba Tinubu damar saka dokar ta baci. Amma kamin a saka dokar ta baci akwai ka'idojin da ake bi. Wasu daga cikin ka'idojin sune kamar haka: Ya zama cewa, Ana yiwa Najeriya barazana ta bangaren jihar daga kasar waje. Ya zama ana fuskantar barkewar yaki. Ya zamana cewa babu doka kowa na abinda ya ga dama. Ya zama cewa, Najeriya na fuskantar rugujewa. Ya zama cewa wani iftila'i kamar girgizar kasa ko Ambaliyar ruwa me muni ta fadawa jihar. Ko kuma wata matsala da ka iya shafar duka Najeriya. ...
Gwamnatin tarayya ta baiwa ‘Yan kasar India dubu 11 aikin kamfanin man fetur me albashi me kauri, Kungiyar ma’aikatan man fetur ta PENGASSAN tace bata yadda ba dole a maidasu kasarsu a baiwa ‘yan Najeriya aikin

Gwamnatin tarayya ta baiwa ‘Yan kasar India dubu 11 aikin kamfanin man fetur me albashi me kauri, Kungiyar ma’aikatan man fetur ta PENGASSAN tace bata yadda ba dole a maidasu kasarsu a baiwa ‘yan Najeriya aikin

Duk Labarai
Kungiyar ma'aikatan man fetur ta PENGASSAN ta zargi ma'aikatar kwadago da ma'aikatar harkokin cikin gida da baiwa 'yan kasar India su kusan dubu 11 damar samun aiki a kamfanin harkar man fetur na Sterling Oil Exploration and Energy Production Company Limited. Shugaban PENGASSAN, Festus Osifo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar inda yace wannan aiki da aka baiwa Indiyawan aikin 'yan Najeriya ne. Dan haka ya bukaci a kwace aikin a baiwa 'yan Najeriya su kuma indiyawan a mayar dasu kasarsu. Yace idan ba'a yi hakan ba, zasu dakatar da ayyukansu sannan zasu shiga gagarumin yajin aiki. Yace ba zai yiyu ana kukan babu aiki a kasa ba a rika dauko 'yan wata kasa da yawa haka ana basu aikin da ya kamata 'yan kasa suke yi ba. Yace dole gwamnati ta zaba ko dai ta goyi bayan '...
Kalli Mutane 10 dake shiga fadar shugaban kasa su ga Tinubu kai tsaye ba tare da shamaki ba, ‘yan Arewa 3 ne kacal a cikinsu

Kalli Mutane 10 dake shiga fadar shugaban kasa su ga Tinubu kai tsaye ba tare da shamaki ba, ‘yan Arewa 3 ne kacal a cikinsu

Duk Labarai
Akwai mutane 10 da basu da shamaki da fadar shugaban kasa inda a koda yaushe zasu iya shiga fadar shugaban kasar su ganshi ba tare da shamaki ba. Wadannan mutane rahoton jaridar Sunnews tace makusanta ne ko kuma ace aminaine na shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Gasu kamar haka: Chief Bisi Akande, Jigo a APC Oba Rilwan Akiolu, watau Sarkin Legas Abdullahi Ganduje Shugaban jam'iyyar APC. Orji Uzor Kalu Abdul’aziz Yari: Tsohon gwamnan Zamfara. Oba Sikiru Kayode Adetona Olusegun Osoba Ibrahim Masari Prince Tajudeen Olusi James Ibori
Kalli Bidiyo:Soja ya bace bayan da ya zargi cewa sojojin da aka jiwa rauni a wajan aiki da kudaden Aljihunsu suke kula da kansu a Asibitoci

Kalli Bidiyo:Soja ya bace bayan da ya zargi cewa sojojin da aka jiwa rauni a wajan aiki da kudaden Aljihunsu suke kula da kansu a Asibitoci

Duk Labarai
Wani karamin sojan Najeriya ya bace bayan da ya bayyana cewa sojojin da aka jiwa rauni da kudaden Aljihunsu suke kula da kawunansu ba hukumar sojin ce ke kula dasu ba. Sojan ya bayyana hakanne a wani bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta. Yace maganar gaskiya ya ji dadi da aka hana shugaban sojoji Visa zuwa kasar Canada, yace da ba'a hanashi Visar ba da ba za'a san cewa turawanne ke daukar nauyin ayyukan ta'addanci ba. Yace yana fatan a ci gaba da hana shuwagabannin sojojin Visa dan Asiri ya tonu 'yan Najeriya su san halin da ake ciki game da matsalar tsaro. Kalli Bidiyon lamarin anan
Kalli Wanda shugaba Tinubu ya nada a matsayin me kula da gudanar da jihar Rivers bayan dakatar da Gwamna Fubara

Kalli Wanda shugaba Tinubu ya nada a matsayin me kula da gudanar da jihar Rivers bayan dakatar da Gwamna Fubara

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa tsohon shugaban sojojin ruwa, Vice Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas mukamin kula da gudanar da jihar rivera bayan da ya dakatar da Gwamna Fubara. A ranar 18 ga watan Maris ne dai shugaban kasar ya dakatar da gwamna Simi Fubara da mataimakinsa da majalisar jihar na tsawon watanni 6 kamin aga abinda hali yayi. Wasu rahotanni sun bayyana cewa, sojoji sun yiwa Gwamna Fubara daurin talala a gidansa tare da iyalinsa.
Falalar Goma na karshe daga bakin Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Falalar Goma na karshe daga bakin Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Duk Labarai
Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na Najeriya kuma shugaban hukumar Hizba ta jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce duk da cewa dukkannin ranaku da dararen watan Ramadan na da falala amma kwanaki 10 na ƙarshen watan sun fita daban. "Goman ƙarshe na da wasu abubuwa guda uku masu muhimmancin kuma wannan ne ma ya sa ake fifita goman ƙarshen a kan goman farko da na tsakiya." In ji Sheikh Daurawa. Allah ya yi rantsuwa da darare 10: Na farko dai Allah ya yi rantsuwa da su inda a cikin Alƙur'ani ya ce Wal Fajr, Wa Layalil A'shar. Malamai sun ce wannan na nuni da kwanakin ƙarshe na Ramadan ko kuma goman farko na watan Zulhijja. Daren Laylatul Qadr ya faɗo a goman ƙarshe: Abu na biyu a cikin wannan watan akwai daren Laylatul Qadr. Idan mutum ya yi dace a daren 21 ko 23 ko ...