Saturday, December 13
Shadow
Da gaske an soke jarabawar WAEC ta 2025 saboda yawan satar amsa? Hukumar jarabawar ta yi karin bayani

Da gaske an soke jarabawar WAEC ta 2025 saboda yawan satar amsa? Hukumar jarabawar ta yi karin bayani

Duk Labarai
Hukumar shirya jarabawar kammala sakandare ta WAEC ta yi martani kan labarin da ke cewa an soke jarabawar ta shekarar 2025. Labarai na ta jawo a kafafen sadarwa inda aka ji wasu na cewa an soke jarabawar ta shekarar 2025. An bayyana cewa an soke jarabawar ne saboda yawaitar satar amsa. Saidai hukumar ta WAEC a Martani kan lamarin tace bata soke jarabawar ba asali ma nan da watan Augusta zata saki sakamakon jarabawar. “The attention of the West African Examinations Council (WAEC), Nigeria, has been drawn to a press statement alleging the cancellation of all the papers written during the just concluded WASSCE for School Candidates, 2025. According to the press statement dated Saturday, July 19, 2025, being circulated on social media platforms, the Federal Ministry of Education, ...
Kotu ta daure mutane 2 a gidan yari saboda sare itace a Kano

Kotu ta daure mutane 2 a gidan yari saboda sare itace a Kano

Duk Labarai
Kotu dake Normansland a Kano ta daure mutane 2 bisa hannu a sare itace a jihar wanda sabawa dokar Muhalli ta jihar ne. Ma'aikatar Muhalli ta jihar, ta sanar da cewa an kama wani me suna Salihu Mukhtar da wani abokin aikinsa da suka sare itace akan titin Jigawa Road dake Nasarawa GRA. Lauya me gabatar da kara, Barrister Bahijjah Aliyu ne ya gayawa kotu cewa wadanda aka kama din sun karya dokar muhalli ta jihar. An yankewa daya daga cikinsu hukuncin daurin watanni 3 a gidan yari ko biyan tarar Naira 20,000. Sannan aka yankewa dayan hukuncin daurin watanni 6 a gidan yari ko biyan tarar Naira dubu 50. Kwamishinan muhalli na jihar, Dr. Dahiru Hashim ya bayyana cewa ba zasu amince da sare itatuwa a jihar ba.
Dala Biliyan $3.6 ‘yan Najeriya suka rika kashewa duk shekara wajan zuwa kasashen waje neman magani a zamanin Buhari

Dala Biliyan $3.6 ‘yan Najeriya suka rika kashewa duk shekara wajan zuwa kasashen waje neman magani a zamanin Buhari

Duk Labarai
.Rahotanni sun ce a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari 'yan Najeriya sun kashe jimullar dala Biliyan $29.29 wajan zuwa kasashen waje neman magani. Hakan na nufin 'yan Najeriya sun rika kashe akalla dala $3.6 duk shekara wajan neman magani a kasashen waje a shekaru 8 da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yi yana mulki. Hakan ya bayyana ne daga bayanan da babban bankin Najeriya, CBN ya fitar. Hakan ya nuna irin yanda 'yan Najeriya suka dogara da kasashen waje wajan neman magani.
Hotuna Da Duminsa: Kwankwaso ya je ganawa da shugaba Tinubu a Abuja

Hotuna Da Duminsa: Kwankwaso ya je ganawa da shugaba Tinubu a Abuja

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Tsohon gwamnan jihar Kano, kuma jigon jam'iyyar NNPP Sen. Rabiu Musa Kwankwaso, yanzu haka yana fadar shugaban kasa domin ganawa shugaban kasa Tinubu
ADC ce ke amfani da rasuwar Buhari don neman karɓuwa ba ji ba>>Shugaba Tinubu

ADC ce ke amfani da rasuwar Buhari don neman karɓuwa ba ji ba>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Fadar Shugaban Najeriya ta mayar da martani kan zargin da jam’iyyar haɗaka ta ADC ta yi na cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu na amfani da rasuwar tsohon shugaba Muhammadu Buhari, don samun tagomashi na siyasa da neman karɓuwa a idon jama'a. Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare ya bayyana zargin na ADC a matsayin “abin kunya,” inda ya ce jam’iyyar ce ke amfani da rasuwar Buhari don neman suna. ADC dai ta ce gwamnatin Tinubu ta yi amfani da yadda aka gudanar da jana’izar Buhari da kuma yadda aka shirya bikin bankwana da shi a Daura da ke jihar Katsina, domin ƙara samun ƙarbuwa a idon ƴan ƙasa. Fadar shugaban ƙasar ta ce marigayi Muhammadu Buhari ya cancanci yi masa jana'izar ban-girma kuma sun yi haka ne don girmamawa saboda hakan ne ya dace da sh...
YANZU-YANZU: An Fara Gudanar Da Zàñga-zàñgar Kan Karin Albashi Da Fanshøɲ ‘Yan Sanda Masu Aiki Da Masu Ritaya

YANZU-YANZU: An Fara Gudanar Da Zàñga-zàñgar Kan Karin Albashi Da Fanshøɲ ‘Yan Sanda Masu Aiki Da Masu Ritaya

Duk Labarai
YANZU-YANZU: An Fara Gudanar Da Zàñga-zàñgar Kan Karin Albashi Da Fanshøɲ 'Yan Sanda Masu Aiki Da Masu Ritaya. Daga Muhammad Kwairi Waziri Yayin wata gagarumar zanga-zanga da aka gudanar a yau, Omoyele Sowore, ɗan gwagwarmaya kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, ya jagoranci gungun masu zanga-zanga domin neman a inganta rayuwar jami’an ‘yan sanda a Najeriya. Masu Zãɲgà-Zàɲģà sun bukaci gwamnati ta duba halin kuncin da ‘yan sanda ke fuskanta, musamman yadda albashinsu ke ƙasa da kima, tare da rashin kula da ‘yan sanda da suka yi ritaya. Sun ce lokaci ya yi da za a mutunta waɗanda ke bayar da rayukansu don kare lafiyar jama’a da dukiyarsu. Sowore ya bayyana cewa, "Yan sanda su ne ginshiƙin tsaro a ƙasa, amma ana wulaƙanta su da iyalansu. Ba za mu ci gaba da shiru ba alhali ...
Kalli Bidiyon: Babban yaron Naziru Sarkin Waka, Abba Csale ya jawo cece-kuce sosai bayan da yace Naira Miliyan 5 bata masa wahalar samu a wata

Kalli Bidiyon: Babban yaron Naziru Sarkin Waka, Abba Csale ya jawo cece-kuce sosai bayan da yace Naira Miliyan 5 bata masa wahalar samu a wata

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"transform":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Babban yaron Naziru Sarkin Waka me suna Abba Csale ya bayyana cewa, idan bai samu kudi sosai ba a wata shine ya samu Naira Miliyan 5. Ya bayyana hakane a yayin da yake magana da wanda yayi tataki daga legas zuwa wajan Sarkin wakan. Saidai da yawa basu yadda da abinda ya fada ba inda suka ce gashi sun ganshi da silifas a Bidiyon sannan sannan kullun da jallabiya daya ake ganinshi. https://www.tiktok.com/@nurullah4676/video/7529147171690532102?_t=ZM-8yCpfYjP...
Wanda ya gayamin nine zanci zabe a 2023 ya sake gayamin nine zan ci zaben 2027>>Inji Shugaba Tinubu

Wanda ya gayamin nine zanci zabe a 2023 ya sake gayamin nine zan ci zaben 2027>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa an gaya masa shine zai ci zaben shekarar 2027. Ya bayyana hakane a yayin da ya je addu'ar 7 ta marigayin basaraken jihar Ogun, Awujale, Oba Sikiru Adetona. Shugaba Tinubu yace a yayin da yake yakin neman zaben shugaban kasa a 2022, ya kaiwa basaraken ziyara inda ya saka masa albarka sannan ya gaya mai cewa shine zai yi nasara a zaben. Sannan yace ya kuma kara gaya mai cewa shine dai zai sake lashe zaben shekarar 2027. Shugaba Tinubu yace amma yanzu gashi ya tafi ya barmu a Duniya.
Kalli Bidiyo: Ina zaman zamana a Abuja na koma Kano, Sauro ya cijeni, Yanzu bani da lafiya>>Inji Gfresh

Kalli Bidiyo: Ina zaman zamana a Abuja na koma Kano, Sauro ya cijeni, Yanzu bani da lafiya>>Inji Gfresh

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, ya koma kano. Saidai yace komawarsa Kano ke da wuya, Sauro ya cijeshi kuma ya kamu da ciwon zazzabin cizon sauro. An ganshi a wani Bidiyo da ya wallafa ana masa Allura. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7529224207654227205?_t=ZM-8yCnVfqnXei&_r=1 https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7529295115966352646?_t=ZM-8yCo6X8ViAq&_r=1 Gfresh dai a baya ya bayyana cewa, yana Abuja da zama a unguwar Asokoro.
Ma’aikata ne suka yi yawa a jihar mu shiyasa muka kasa biyan mafi karancin Albashi na 70,000 inji Gwamnan Borno, Zulum

Ma’aikata ne suka yi yawa a jihar mu shiyasa muka kasa biyan mafi karancin Albashi na 70,000 inji Gwamnan Borno, Zulum

Duk Labarai
Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya bayyana cewa, ma'aikata sun yi yawa a kananan hukumomin jihar Borno shiyasa ya kasa fara biyan ma'aikatan kananan hukumomin mafi karancin Albashi na Naira 70,000. Gwamnan yace akwai ma'aikata 90,000 a kananan hukumomi 27 dake fadin jihar wanda yace sun yi yawa shiyasa ya kasa fara biyansu mafi karancin Albashi na Naira 70,000. Hakan na zuwa ne kusan shekara daya tun bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa wabuwar dokar karin albashi ta mafi karancin Albashi zuwa Naira 70,000 a ranar July 29, 2024. Gwamnan ya bayyana hakane ta bakin babban sakatare a ma'aikatar kananan hukumomi ta jihar Modu Mustapha yayin wani taro a gidan gwamnatin jihar Borno. Yace jihar Kano ta fisu yawa sosai amma ma'aikatan kananan hukumomin ta basu ...