Bincike ya samu Ministan kimiyya na Najeriya da ‘mallakar takardun boge’
Wani bincike da jaridar Premium Times ta yi ya nuna cewa ana zargin ministan kimiyya da fasaha na Najeriya, Uche Nnaji, da yin takardun kammala karatu na boge, lamarin da ke ci-gaba da janyo cece-kuce a ƙasar.
Binciken da jaridar ta Premium times ta wallafa ya ce an gano cewa ministan ya miƙa takardun bogin ga majalisar dattawan ƙasar domin tattance shi, bayan shugaban Bola Ahmed Tinubu ya miƙa sunansa cikin waɗanda yake so ya bai wa muƙamin minista a shekarar 2023.
Jaridar ta yi ikirarin cewa takardun shaidar kammala karatun digiri da na bautar ƙasa na Mr Nnaji duka na boge ne.
Inda ta ƙara da cewa masu suka sun ce ministan bai kammala karatun digirin ba, haka kuma takardar shaidar bautar ƙasar da ya miƙa wa ofishin sakataran gwamnatin tarayya da hukumar tatta...








