Tauraron Fina-finan Hausa, Adam A. Zango kenan tare da Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Salihu Alkali Zariya a kasa me tsarki.
An ga Adam A. Zango yana musu hotunan Selfie.
Wani mutum dan kasar Turkiyya da shan taba yawa katutu ya rasa yanda zai yi ya kulle kansa a cikin keji dan ya daina wannan dabi'a.
Mutumin me suna Ibrahim Yucel, bayan ya kulle kansa ya baiwa matarsa makullin inda take budeshi kawai idan zai ci abinci.
Saidai zuwa yanzu ba'a san ko hakan ya taimaka masa wajan cimma burinsa ba.
Rahotanni sun bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne bayan da cutar dajin huhu ta kashe mahaifinsa.
Shugaban 'yansandan Najeriya, IGP Kayode ya bayar da umarni ga 'yansandan kasarnan da su daura bakin kyalle na tsawon kwanaki 7 dan nuna alhinin rasuwar shugaban sojoji Lt. Gen. Taoreed Lagbaja.
Kakakin 'yansandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai.
Yace wannan matakine da aka dauka dan girmama tsohon shugaban sojojin da kokarin da ya nuna wajan yaki da matsalar tsaro.
Gwamnatin Tarayya ta yiwa 'yan Najeriya godiya bisa hakurin da suke yi da matsin rayuwa da suka shiga saboda tsare-tsaren gwamnatin.
Hakan ya fito ne daga bakin ministan kudi, Wale Edun inda yake ganawa da 'yan majalisar tarayya.
Yace 'yan Najeriya sun cancanci yabo bisa hakuri da juriya da suka nuna inda gashi yanzu har an kawo matakin moriyar wadannan gyare-gyaren.
Ministan yace manya-manyan gyare-gyaren da suka yi sune cire tallafin man fetur da cire tallafin dala wanda kuma yanzu an fara ganin nasarar wannan mataki nasu.
Rundunar tsaron Najeriya ta tabbatar da ɓullar ƙungiyar lakurawa waɗanda suke tayar da zaune tsaye a tsakanin jihohin Sokoto da Kebbi.
Daraktan watsa labarai na hedkwatar ne ya tabbatar da hakan a Abuja, kamar yadda kafofin watsa labarai suka ruwaito, inda ya ƙara da cewa suna da tabbacin ɓullar ƙungiyar a Sokoto da Kebbi.
Sai dai ya ƙara cewa ƙungiyar ba za ta yi wani tasiri ba, domin a cewarsa sojojin Najeriya a shirye suke, kuma za su ga bayansu cikin ƙanƙanin lokaci.
Lakurawa wata ƙungiya ce ta ƴanbindiga da suka fara addabar mutanen Sokoto da Kebbi, kuma sun fito ne daga ɓangaren yankin Sahel da ya ƙunshi ƙasashen Nijar, da Mali, kuma mutane ne da suka ƙunshi ƙabilu daban-daban na Sahel.
A jihar Kano, ƙungiyar likitoci ta umarci likitocin jihar su koma bakin aiki bayan janye yajin aikin da aka wayi gari da shi a asibitin ƙwararru na Murtala Muhammad a ranar Alhamis.
Likitocin dai sun shiga yajin aikin ne bayan cikar wa’adin sa’o’i 48 da ƙungiyar ta baiwa gwamnan jihar, na ya kori kwamishiniyar jin ƙai ta jihar, Amina Abdullahi HOD, bisa zargin cin zarafin wata likita a asibitin, zargin da ta ce musanta. Duk da cewa likitocin sun janye yajin aikin amma ƴan sa’o’in da aka shafe babu likitoci a asibitin na Murtala Muhammad har an ga tasirinsa, inda ya shafa majinyata.
Wani rahoto da aka fitar ya nuna cewa yunwar da ake fama da ita a Najeriya zai iya tsananta a shekarar 2025, inda aka yi hasashen cewa aƙalla mutum miliyan 33 ne za su iya shiga yunwa a shekarar ta baɗi.
Ƴan Najeriya a yanzu sun kai kusan miliyan 223.8.
A rahoton, wanda Cadre Harmonisé ta yi a ƙarƙashin kulawar gwamnatin tarayya, da haɗin gwiwar shirin samar da abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya ne ya bayyana hakan, inda rahoton ya yi hasashen cewa ƴan ƙasar aƙalla miliyan 33.1 ne za su fuskanci yunwa.
Rahoton ya ta'allaƙa hasashen ne kan yanayin taɓarɓarewar tattalin arzikin ƙasar da hauhawar farashin kayayyaki da sauyin yanayi da rikce-rikice a wasu yankuna na arewacin ƙasar.
Rahoton ya ƙara da cewa tsakanin Oktoba zuwa Disamban 2024, kimamin mutum miliyan 25.1 ake hasashen za...
Gwaska ya kara da cewa, yanzu gidajen mai har kiran kwastoma suke ya zo ya sai mai, sabanin lokacin mulkin Obasanjo da kokawa ake shan mai.
Gashi kuma an yaki 'yan ta'àdda da țà'addanci. Don haka mu kara zabar Tinubu don cigaban Nijeriya"
Me za ku ce?
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar Ya Naɗa Babban Malamin Addinin Musulunci, Farfesa Mansur Sokoto Sarautar Danmasanin Daular Usmaniyya
Allah Ya Taya Riƙo!
Wasu 'yan Najeriya sun taru inda suka yi bikin murnar cin zaben shugaban kasar Amurka Donald Trump.
Mutanen wadanda kiristocine sun rika yima Trump fatan samun Nasara.
Ko da kamin zaben dai, An samu wasu mutane na yiwa Trump Addu'a lr Allah ya bashi nasara.