Monday, December 15
Shadow
Ashe wannan bodiyon da aka rika yadawa cewa wai an kama wata ta je binne wani abu a kabari karyane shiryawa kawai aka yi dan batawa mutane lokaci, Kalli Bidiyon yanda abin ya faru

Ashe wannan bodiyon da aka rika yadawa cewa wai an kama wata ta je binne wani abu a kabari karyane shiryawa kawai aka yi dan batawa mutane lokaci, Kalli Bidiyon yanda abin ya faru

Duk Labarai
A makon da ya gabata ne dai aka rika yada Bidiyon wata mata da cewa wai ta je binne wani abune a kabari aka kamata. Saidai daga baya an rika sukar wadda ta yada Bidiyon da cewa ta tozarta wadda aka kama da laifin. Bayan gano hakanne dai aka rikawa wanda wadda ta yada abin tofin Allah tsine inda wasu ma ke cewa ya kamata a kamata wasu ma na cewa a kasheta, kamar yanda take fada. Saidai wadda ta dauki bidiyon ta fito ta bada hakuri. https://www.tiktok.com/@aliyuzakiru1/video/7530047652168240389?_t=ZM-8yGcJjNseNc&_r=1 Ko wane mataki kuke ga ya kamata a dauka?
Da Duminsa: Wike ya gayawa shugaba Tinubu wata maganar da bata kamata ba kuma maganar ta fito, ji abinda yace

Da Duminsa: Wike ya gayawa shugaba Tinubu wata maganar da bata kamata ba kuma maganar ta fito, ji abinda yace

Duk Labarai
Rahotanni sun ce ministan Abuja Nyesom Wike ya fadi abinda bai kamata ba akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ana ganin Wike a matsayin na hannun damar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu wanda ke abinda ya ga dama a gwamnatin Tinubu ba tare da an taka masa burki ba. A kwanannan aka ruwaito cewa Wike ya baiwa 'ya'yansa biyu filaye masu yawa a Abuja. Hakanan kuma ya baiwa iyayensa da 'yan uwa filayen. A wani sabon labari da jaridar Peoplesgazette ta ruwaito, tace Wike yace babu abinda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai masa. Sannan babu wani alkalin da ya isa ya daureshi a Najeriya. Hakan na zuwane bayan da ake kira ga shugabab kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauki mataki akan yanda Wike ke abinda ya ga dama a Gwamnatinsa.
An sallami gwamna Dikko Raɗa daga asibiti

An sallami gwamna Dikko Raɗa daga asibiti

Duk Labarai
An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, daga asibiti bayan an tabbatar da ya samu sauƙi daga raunin da ya samu sakamakon hatsarin mota a hanyarsa daga Katsina zuwa Daura. Gwamnan ya samu kulawa ta musamman daga masana lafiya, kuma yanzu an tabbatar da cewa ya dace da komawa bakin aiki ba tare da wata matsala ba. A cewar wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan, Ibrahim Kaula Mohammed ya fitar, likitan da ke kula da lafiyar gwamnan ya tabbatar da cewa ya samu sauƙi sosai, kuma ya shirya tsaf don ci gaba da gudanar da ayyukan mulkinsa. Bayanin da gwamnatin jihar dai ta fitar game da hatsarin ta ce lamarin ya faru ne a lokacin da gwamna Radda ke kan hanyarsa ta zuwa Daura, inda wata mota ƙirar Golf ta kauce hanyarta, kuma ta faɗa wa motar da gwamnan...
Buhari yanzu ya manta da duk wani dadi da ya taba ji>>Inji Gfresh

Buhari yanzu ya manta da duk wani dadi da ya taba ji>>Inji Gfresh

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, akwai tashin hankali tattare da mutuwa, inda yace yanzu fa Buhari ya manta da duk wani jin dadi da ya taba yi. Gfresh ya bayyana hakane a shafinsa na Tiktok inda yace yaso ace ana shekaru 8 kamin a mutu https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7530036370635640070?_t=ZS-8yGMfHm5z4j&_r=1
Kalli Bidiyon: Aljanin da ya aureni ya sakeni, na gaji da zaman zawarci>>Murja Kunya

Kalli Bidiyon: Aljanin da ya aureni ya sakeni, na gaji da zaman zawarci>>Murja Kunya

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Murja Kunya ta bayyana cewa, Aljanin da ya aureta ya saketa. Ta kata da cewa ta gaji da zaman zawarci da kwana ita kadai. Murja ta bayyana hakane a sabon Bidiyon da ta saki inda tace kamin mutum ya ankara sai ya ga yayi soyayya da maza kusan 20 duk inda ka wuce ana nunaka saboda sun sanka. https://www.tiktok.com/@murjakunya0/video/7530173534421748997?_t=ZS-8yGJZU7UV6H&_r=1
Gwamnatin tarayya ta warewa jama’ar jihar Bayelsa da Rivers tallafi da bashin Naira Miliyan 200, sai rokonsu ake su je su karba

Gwamnatin tarayya ta warewa jama’ar jihar Bayelsa da Rivers tallafi da bashin Naira Miliyan 200, sai rokonsu ake su je su karba

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta warewa jama'ar jihohin Rivers da Bayelsa bashi me hade da tallafi na Naira Miliyan 200 ta hanyar bankin manoma na tarayya watau BOI. Kowacce jiha a cikin jihohin biyu an ware mata Naira Miliyan 100. Saidai mutanen jihar basa zuwa karbar wannan bashi, dalili kenan da yasa bankin na BOI ya nuna damuwa hadi da kiran cewa mutanen wadannan jihohi su zo su nemi wannan bashi. Shugaban bankin na yankin Pacqueens Irabor ne ya bayyana hakan inda yace mutum daya zai iya neman bashin Naira Miliyan 10 kuma za'a biya bashin ne nan da shekaru 3. Yace kaso 40 cikin 100 na bashin tallafi ne, kaso 60 ne kawai mutum zai biya. Yayi kira ga 'yan kasuwa da kananan masana'antu da su je su karbi wannan bashi.
Majalisar tarayya na shirin yin sabuwar dokar da zata hana ma’aikatan Gwamnati saka ‘ya’yansu makarantar kudi da zuwa asibitin kudi

Majalisar tarayya na shirin yin sabuwar dokar da zata hana ma’aikatan Gwamnati saka ‘ya’yansu makarantar kudi da zuwa asibitin kudi

Duk Labarai
Majalisar wakilai na shirin yin sabuwar dokar da zata hana ma'aikatan gwamnati da 'yan siyasa zuwa Asibitin kudi da saka 'ya'yansu makarantun kudi. Zasu dauki wannan mataki ne dan farfado da Kimar ma'aikatun gwannatin. Dan majalisar, Hon. Amobi Godwin Ogah ne ya gabatar da kudirin a ranar Talata. Yace amfani da Asibitoci da makarantun gwamnati da ma'aikatan gwamnati da 'yan siyasa ke yi ne yasa na Gwamnatin ke lalacewa. Ya nemi goyon bayan wannan sabon kudiri daga 'yan Jarida dama sauran 'yan Najeriya.
Bamu Amince da kirkirar sabbin jihohi ba>>Majalisar Dattijai

Bamu Amince da kirkirar sabbin jihohi ba>>Majalisar Dattijai

Duk Labarai
Majalisar Dattijai ta Najeriya tace bata amince da kirkirar sabbin jihohi ba. Kakakin Majalisar, Godswill Akpabio ne ya bayyana hakan. Hakan na zuwane bayan da labarai a kafafen sada zumunta suka yadu cewa majalisar ta amince da kirkirar sabbin jihohi. Sanata Senator Abdul Ningi ne ya kai maganar majalisar inda Akpabio yace tabbas an gabatar musu da neman kirkira jihohi 42 amma basu amince da maganar ba tukuna. Akpabio yace mutane su rika bin labaran da majalisar kadai ta wallafa sahohai.