Sunday, March 1
Shadow
Mutanen Kaduna sun ki fitowa su tarbi Tinubu shine suka samo yara ‘yan makaranta suka zuba akan Titi>>Inji Tsohuwar Hadimar Shagaban kasa, Lauretta Onochie

Mutanen Kaduna sun ki fitowa su tarbi Tinubu shine suka samo yara ‘yan makaranta suka zuba akan Titi>>Inji Tsohuwar Hadimar Shagaban kasa, Lauretta Onochie

Duk Labarai
Tsohuwar hadimar shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Lauretta Onochie ta bayyana cewa, ziyarar da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kai jihar Kaduna bata yi Armashi ba. Ta godewa mutanen Kaduna saboda kin fitowa su tarbi shugaban kasar inda tace sai yara aka samo aka zuba akan titi. Ta bayyana hakane a shafinta na X. Ta kara da cewa, wannan sakamakon mulki da rashin bin doka kenan. https://twitter.com/Laurestar/status/1969161660553187344?t=S78sFGCVGhA-gpmwqQO5iA&s=19
Ka wallafa Sunayen mutanen da Gwamnatinka tace ta baiwa Tallafin Naira dubu ashirin da biyar duk wata>>Kungiyar Yarbawa ga Shugaba Tinubu

Ka wallafa Sunayen mutanen da Gwamnatinka tace ta baiwa Tallafin Naira dubu ashirin da biyar duk wata>>Kungiyar Yarbawa ga Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Wata Kungiyar Yarbawa me suna Ìgbìnmó Májékóbájé Ilé-Yorùbá ta bukaci shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya wallafa sunayen mutanen da gwamnatinsa tace ta rika baiwa tallafin Naira dubu 25 duk wata. Kungiyar ta bakin shugabanta, Olusola Badero tace wannan maganar duk farfaganda ce. Tace ko da da gaske an bayar da wannan tallafin, idan aka duba, za'a ga cewa yawanci 'yab jam'iyyar APC ne. Tace dan haka a wallafa sunayen mutanen da aka baiwa tallafin da jihohin da suka fito. Kungiyar tace ko da ma an bayar da tallafin da gaske, Naira 25,000 a wata ba zata iya ciyar da iyali ba, saboda buhun shinkafa ya haura Naira 70,000. Kumgiyar tace tun da shugaba Tinubu ya hau mulki mutane a shiyyar Yarbawa suka fada yunwa da talauci inda da yawa sun koma roko kamin su samu abinci....
Kalli Bidiyon dandazon jama’ar da suka Tarbi Shugaba Tinubu a Kaduna, wasu sun ce ko Buhari sai haka

Kalli Bidiyon dandazon jama’ar da suka Tarbi Shugaba Tinubu a Kaduna, wasu sun ce ko Buhari sai haka

Duk Labarai
Mutane da yawa ne suka fito suka tarbi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a ziyarar da ya kai Jihar Kaduna. Shugaba Tinubu ya je jihar Kadunane halartar daurin auren dan sanata Abdulaziz Yari, sannan ya kaiwa matar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari watau Hajiya A'isha Ziyara. https://twitter.com/HBMayana_/status/1969121724374409254?t=f8p24RUXvNk9tsGG1mvYjQ&s=19
Kalli Bidiyon ganawar Shugaba Tinubu da Sule Lamido a Kaduna duk da cewa jam’iyyar su ba daya ba, Bidiyon ya dauki hanka

Kalli Bidiyon ganawar Shugaba Tinubu da Sule Lamido a Kaduna duk da cewa jam’iyyar su ba daya ba, Bidiyon ya dauki hanka

Duk Labarai
Bidiyon ganawar tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a Kaduna wajan daurin auren dan Sanata Abdulaziz Yari ya dauki hankula sosai. A Bidiyon an ga yanda shugaba Tinubu ya mike tsaye suka gaisa da Sule Lamido, da yawa sun rika cewa, siyasa ba da gaba ba. https://twitter.com/SundayDareSD/status/1969057168813916623?t=mLmxEJAPOBEuRaLdNB-1yw&s=19
Kalli Bidiyon: Wallahi, Wallahi, Wallahi ban taba yin Zynq ba amma wata matar aure ta yaudareni na aikata alfasha da ita

Kalli Bidiyon: Wallahi, Wallahi, Wallahi ban taba yin Zynq ba amma wata matar aure ta yaudareni na aikata alfasha da ita

Duk Labarai
Wani matashi ya aikawa Sheikh Abdulfatahi Gadon kaya wasika inda yace wata matar aure ta yaudareshi sun aikata zina. Yace shi bai taba aikatawa ba, wannan ne karon farko. Yace ji yake kamar ya fita daga Musulunci. Ya nemi malam ya bashi shawarar yanda zai tuba. https://www.tiktok.com/@nijar.maradi.gida3/video/7548918678033566983?_t=ZS-8zrYVtw6V9M&_r=1
Kalli Bidiyon Sultana ta BBNaija dake ikirarin ita Musulmace daga Arewa, yanda ta, chire kayan jiqinta, ta yi Tumbur Haihuwar uwarta a tsakiyar ‘yan BBNaija din, ta sake jawo cece-kuce sosai, da yawa na cewa suna kokwanton Musuluncin ta

Kalli Bidiyon Sultana ta BBNaija dake ikirarin ita Musulmace daga Arewa, yanda ta, chire kayan jiqinta, ta yi Tumbur Haihuwar uwarta a tsakiyar ‘yan BBNaija din, ta sake jawo cece-kuce sosai, da yawa na cewa suna kokwanton Musuluncin ta

Duk Labarai
Tauraruwar BBNaija, Sultana wadda 'yar Asalin Jihar Adamawa ce ta sake jawo cece-kuce. Sultana ta jawo cece-kuce ne bayan Bidiyon ta da aka ga tana rawa tsirara a gaban abokanta da suke yin BBNaija din tare. Wasu dai musamman daga kudu sai jinjina mata suke suna cewa ta iya rawa amma wasu na mamakin ashe dama 'yan matan Arewa sun iya sheke aya haka? https://twitter.com/wendysmith2468/status/1968821971950489994?t=zlPysUOLNXZLrp2IfR6fLA&s=19 https://twitter.com/_sultanafarida/status/1968822203182379416?t=uvXqzJ3TUEQQcl95uEkNCg&s=19 Sultana dai ta taba bayar da labarin cewa mahaifinta Musulmine amma mahaifiyarta kirista ce daga kudancin Najeriya. Tace ta taso tana Sallah kuma tana zuwa coci amma dai daga baya ta zabi ta zama musulma.
Kalli Bidiyon: Shugaba Tinubu ya je gaishe da matar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, watau A’isha a Kaduna

Kalli Bidiyon: Shugaba Tinubu ya je gaishe da matar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, watau A’isha a Kaduna

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya je gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari inda ya gaishe da matarsa, A'isha. Shugaban ya gaishe da A'isha ne inda yace mata zai ci gaba da tabbatar da irin tsare-tsaren shugaban kasa, Muhammadu Buhari. https://twitter.com/Abdool85/status/1969016925066858995?t=6E_jyQ2Plu96hHwEVx-jLA&s=19
Bayan na Farko, Matatar Man fetur din Dangote ta sake aika Jiragen Ruwa uku dauke da Gas zuwa kasar Amurka

Bayan na Farko, Matatar Man fetur din Dangote ta sake aika Jiragen Ruwa uku dauke da Gas zuwa kasar Amurka

Duk Labarai
Rahotanni sun ce matatar man fetur din Dangote ta sake aikewa da Manyan Jiragen ruwa dauke da Gas zuwa kasar Amurka. Hakan na zuwane bayan na farko da matatar ta kai kasar. Rahotannin sun ce kasar Amurka ta bayyana cewa, Gas din da matatar man fetur din Dangote ke fitarwa na da ingancin da kasar ke bukata. A baya dai mutane da yawa sun yi mamakin jin yanda matatar man fetur din Dangoten ta yi nasarar fara fitar da man fetur zuwa kasar Amurka.