Wednesday, March 4
Shadow
Kalli Bidiyon: Diyar tsohon Gwamnan Kano, Balaraba Ganduje ta bayar da Naira Miliyan 10 a wajan bude shagon kwalliya na Tauraruwar fina-finan Hausa Rashida Mai Sa’a

Kalli Bidiyon: Diyar tsohon Gwamnan Kano, Balaraba Ganduje ta bayar da Naira Miliyan 10 a wajan bude shagon kwalliya na Tauraruwar fina-finan Hausa Rashida Mai Sa’a

Duk Labarai
Diyar tsohon gwamnan Kano, Hajiya Balaraba Ganduje, ta bayar da gudummawar Naira Miliyan 10 a wajan bude shagon kwalliya na Tauraruwar fina-finan Hausa, Rashida Mai sa'a. An ga Hajiya Balaba na bayyana hakane a cikin sabon shagon na Rashida Mai Sa'a. https://www.tiktok.com/@sardunan_matasan_gwoza/video/7541067415883353351?_t=ZS-8z5Z0D4RgsC&_r=1
Dole Tinubu ya dauki mataimaki Kirista ko kuma ya fadi zabe a 2027>>Inji Wata Kungiyar Kirista

Dole Tinubu ya dauki mataimaki Kirista ko kuma ya fadi zabe a 2027>>Inji Wata Kungiyar Kirista

Duk Labarai
Wata kungiya me suna Northern Ethnic Nationality Forum ta yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu barazanar faduwa zabe muddin bai daiki mataimaki Kirista ba. Kungiyar ta bakin shugabanta,Dominic Alancha ta jawo hankalin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da cewa, kada ya maimaita kuskuren sake zabar Muslimi a matsayin abokin takararsa a 2027. Alancha yace dolene Tinubu ya dauki mataimaki Kirista daga daya daga cikin jihohin Plateau, Benue, ko Taraba dan kaucewa tunanin da akewa gwamnatinsa na son mayar da Najeriya kasar Musulmi. Sun yi gargadin cewa, sakw daukar musulmi a matsayin mataimaki, zai sa 'yan Adawa su yi nasara.
Buhari ba mutum bane irin mu, wani na musamman ne daga Allah ya zo da siffar mutane>>Inji Bisi Akande

Buhari ba mutum bane irin mu, wani na musamman ne daga Allah ya zo da siffar mutane>>Inji Bisi Akande

Duk Labarai
Buhari wani Mala'ika ne da ya zo a siffar mutane - Akande Chief Bisi Akande mai mallakin jam'iyyar APC Kuma tsohon Gwamnan Jihar Osun ya yi ta'aziyyar rasuwar marigayi tsohon shugaban ƙasar Najeriya Muhammad Buhari, inda ya ayyana shi a matsayin wani Mala'ika ne da ya zo da jikin mutum, wanda ya bar tarihi a Najeriya. Akande ya jagoranci tawagar manyan ƴan siyasa zuwa Kaduna domin yin ta'aziyya ga iyalan sa, yana mai bayyana damuwa ga rasuwar tsohon shugaban ƙasar. Da yake bayyana ganin shi na ƙarshe na tsohon shugaban ƙasar a Daura, Bisi Akande ya gansa da lafiyar sa da ƙwarin sa, wanda ya nuna babu wata alamar rashin lafiya, wanda ya nuna mutuwa dole ce ga kowa.
Shugaban Sojojin Najeriya ya bayyana masu daukar nauyin matsalar tsaro da abinda suke son cimmawa a Najeriya

Shugaban Sojojin Najeriya ya bayyana masu daukar nauyin matsalar tsaro da abinda suke son cimmawa a Najeriya

Duk Labarai
Shugaban hedikwatar tsaro ta kasa, Christopher Musa ya zargi cewa, yawaitar matsalar tsaron da ake fama da ita a Najeriya na da alaka da gabatowar zaben 2027. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. Yace idan ba haka ba, ta yaya, shekarar data gabata an samu rahoton raguwar matsalar tsaro sosai amma a wannan shekarar abubuwa su kara dagulewa? Yace 'yan siyasa ne ke daukar nauyin 'yan Bindigar inda ya kara dacewa abinda suke son cimma shine bata sunan Gwamnati ace bata kokari. Yace amma abin takaici shine ta yaya zaka rika kashe mutanen da kake son mulka? Ya kuma zargi cewa, bayan masu daukar nauyin 'yan Bindigar a cikin gida, akwai kuma masu daukar nauyin 'yan Bindigar daga kasashen waje.
Gwamnatin Tarayya za ta fara daukar ma’aikatan Hukumar Tsaron Daji (Forest Guards) – Ribadu, Ji karin bayanin yanda za’a dauki aikin

Gwamnatin Tarayya za ta fara daukar ma’aikatan Hukumar Tsaron Daji (Forest Guards) – Ribadu, Ji karin bayanin yanda za’a dauki aikin

Duk Labarai
Mai ba wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce Gwamnatin Tarayya ta fara aiwatar da tsarin daukar ma’aikata karkashin shirin Masu Tsaron Daji (Forest Guards) a matsayin wani bangare na yaki da matsalolin tsaro a karkashin shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Tinubu. Ribadu ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Laraba yayin kaddamar da sababbin motocin aiki 46 da aka raba wa sassan tsaro daban-daban a fadin kasar nan. Ya ce tsarin zai baiwa kowace jiha damar daukar ma’aikata tsakanin 2,000 zuwa 5,000 gwargwadon karfin su. Ya ce shirin zai taimaka wajen kare al’ummomi, dazuzzuka da albarkatun kasa na Najeriya. Ribadu ya kara da cewa akwai sauye-sauye masu ma’ana da ake samu kullum a fannin tsaro, wadanda koda ba su fito fili ba, ana ganin tasirinsu a ra...
Ganduje ya dawo daga London bayan ya shafe wata domin neman lafiya

Ganduje ya dawo daga London bayan ya shafe wata domin neman lafiya

Duk Labarai
Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje, ya dawo Najeriya daga Landan a jiya Laraba. Tsohon gwamnan jihar Kanon ya tafi ƙasar Birtaniya domin neman magani jim kaɗan bayan murabus ɗinsa daga shuagabancin jam'iyya mai mulki a ƙasar. Da ya ke tabbatar da wannan batu ga jaridar The PUNCH, tsohon shugaban ma’aikatansa, Mohammed Garba, ya ce Ganduje ya sauka a Nijeriya ne a safiyar jiya Laraba bayan shafe kusan wata guda a waje. “Eh, ya dawo Najeriya yau. Ya dawo cikin koshin lafiya, kuma ya ƙarasa gidansa,” in ji Garba, yayin da ya ke tabbatar wa da jaridar PUNCH. Ya ƙara da cewa Ganduje ya bar Najeriya zuwa Landan ne kwana biyar bayan ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar domin neman lafiya.